Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Ga Alamu Jakuna Za Su Bace A Doron Kasa Nan Da Shekaru 5
Published: December 9, 2025 at 4:24 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Hukumar kula da rayuwar dabbobi ta majalisar dinkin duniya da masu kare hakkin dabbobi na Afurka sun nuna damuwa ga yanda Jakuna ke matukar raguwa a duniya, saboda kashe su da a ke yi don samun nama da kuma amfani da fatar su wajen magani da ‘yan kasar Sin ke amfani da shi.

A gaba daya duniya alkaluma da aka yi amfani da wata na’ura, na nuni da cewar akwai kimanin Jakuna miliyan 40 a doron kasa.

Lamarin ya ta’azzara bayan ‘yan kasar Sin sun zuba jarin fataucin Jakuna a Najeriya don amfani da fatar Jakin.

Hakan ya haddasa tashin gauron zabi na jakuna da kuma barazanar karar da su har da rahoton shigo da naman bayan sayar da fatar Abuja a soyawa jama’a a matsayin naman yau da kullum.

Tsohon dan majalisar wakilan Najeriya mai sha’awar lamuran kare dabbobi daga cutarwa, Garba Datti Muhammad, ya ce nan da shekara 5 matukar ba a dau matakan da su ka dace ba, Jakuna za su kare a duniya.

Garba Datti wanda ya gabatar da babban jawabi a taron hukumar kula da dabbobi ta majalisar dinkin duniya da ta Afurka, ya ce wasu kan yanka jakuna don amfani da fatar ko cin naman maimakon amfani da jakunan ga lamuran sufuri a karkara.

Datti ya kara da cewa yanzu a duk duniya kimanin Jakuna miliyan 40 a ke da su kuma a na cigaba da hallaka su da cutar da su ba tare da kula da lafiyar su ko gudunmawar da su ke bayarwa ga tattalin arziki ba.

Game da barazanar sayarwa jama’a naman da a ka haramta yankawa na jakuna, wasu manyan makiyaya sun fara tunanin bude mayankar zamani a manyan biranen Najeriya.

Isa Tafida Mafindi tuni ya kafa irin wannn mayankar da ta lashe Naira miliyan dubu goma sha biyar.

Wani abun takaici shi ne yanda mutane ke barin jakuna su hau manyan hanyoyi da dare da kwatsam mai tuka mota sai ya yi kicibis da jaki a tsakiyar titi da kan haddasa mummunan hatsari.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/12/AS-DONKEYS-SEEM-TO-ON-VERGE-OF-EXTERMINATION-1.mp3
Labarai

Post navigation

Previous Post: Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Tura Sojoji Benin
Next Post: Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Da Tarayyar Turai Sun Fidda Sanarwa Afrika
Kungiyoyin Mata A Jihar Filato Sunyi Gangamin Samun Jagorancin Siyasa Afrika
Amurka Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashe Hudu Domin Inganta Kiwon Lafiya Labarai
Kasar Ghana Ta Umarci ‘Yan Kasar Su Daina Zuba Jari A Kasashen Waje Afrika
Wasan Hamayya (Istanbul Derby) Fenerbahçe Da Galatasaray 1-1 Labarai
Kasar Colombia Tare Da Amurka Zasu Fitar Da Man Venezuela Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ana Cigaba Da Samun Hare Hare Da Jiragen Marasa Matuki A Sudan Labarai
  • Shugabannin Kasashen Afirka Ta Tsakiya Sun Kamallah Taron Koli Afrika
  • Malaman Addinin Musulunci Da Kirista Sunyi Bikin Cika Shekara 15 Na Iftar A Najeriya Afrika
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Sojoji Da Fararen Hula A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce! Najeriya
  • Gwamnan Jihar Gombe Ya Umurci A Rufe Makarantu Labarai
  • Majalisar Dattawan Amurka Ta Amince Da Wata Doka Amurka
  • Habasha Tafara Gina Filin Jirgin Sama Mafi Girma A Afirka Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.