Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Amurka Tayi Barazanar Zata Rage Tallafin Da Take BayarwaSudan Ta Kudu, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Ga Alamu Jakuna Za Su Bace A Doron Kasa Nan Da Shekaru 5
Published: December 9, 2025 at 4:24 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Hukumar kula da rayuwar dabbobi ta majalisar dinkin duniya da masu kare hakkin dabbobi na Afurka sun nuna damuwa ga yanda Jakuna ke matukar raguwa a duniya, saboda kashe su da a ke yi don samun nama da kuma amfani da fatar su wajen magani da ‘yan kasar Sin ke amfani da shi.

A gaba daya duniya alkaluma da aka yi amfani da wata na’ura, na nuni da cewar akwai kimanin Jakuna miliyan 40 a doron kasa.

Lamarin ya ta’azzara bayan ‘yan kasar Sin sun zuba jarin fataucin Jakuna a Najeriya don amfani da fatar Jakin.

Hakan ya haddasa tashin gauron zabi na jakuna da kuma barazanar karar da su har da rahoton shigo da naman bayan sayar da fatar Abuja a soyawa jama’a a matsayin naman yau da kullum.

Tsohon dan majalisar wakilan Najeriya mai sha’awar lamuran kare dabbobi daga cutarwa, Garba Datti Muhammad, ya ce nan da shekara 5 matukar ba a dau matakan da su ka dace ba, Jakuna za su kare a duniya.

Garba Datti wanda ya gabatar da babban jawabi a taron hukumar kula da dabbobi ta majalisar dinkin duniya da ta Afurka, ya ce wasu kan yanka jakuna don amfani da fatar ko cin naman maimakon amfani da jakunan ga lamuran sufuri a karkara.

Datti ya kara da cewa yanzu a duk duniya kimanin Jakuna miliyan 40 a ke da su kuma a na cigaba da hallaka su da cutar da su ba tare da kula da lafiyar su ko gudunmawar da su ke bayarwa ga tattalin arziki ba.

Game da barazanar sayarwa jama’a naman da a ka haramta yankawa na jakuna, wasu manyan makiyaya sun fara tunanin bude mayankar zamani a manyan biranen Najeriya.

Isa Tafida Mafindi tuni ya kafa irin wannn mayankar da ta lashe Naira miliyan dubu goma sha biyar.

Wani abun takaici shi ne yanda mutane ke barin jakuna su hau manyan hanyoyi da dare da kwatsam mai tuka mota sai ya yi kicibis da jaki a tsakiyar titi da kan haddasa mummunan hatsari.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/12/AS-DONKEYS-SEEM-TO-ON-VERGE-OF-EXTERMINATION-1.mp3
Labarai

Post navigation

Previous Post: Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Tura Sojoji Benin
Next Post: Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC

Karin Labarai Masu Alaka

Sojoji Sun Murkushe ‘Yan Bindiga A Jihar Sakkwato Labarai
Guterres: Babban Kuskure Ne Yadda Isra’ila Ta Kai Farmaki A Gaza Labarai
An Samar Da Dala Kusan Biliyan Biyu Don Yakar Polio Labarai
Yarjejeniyar Britaniya Da Mauritius Kan Tsibiran Chagos Cin Zarafi Ne Labarai
Gwamna Zulum: Ya Bukaci Sojoji Su Cigaba Da Yakar Boko Haram Da ISWAP Labarai
Mizanin Tattalin Arzikin Najeriya Na 2024 Ya Karu Da Kashi 3.84% Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike a Tituna
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakuncin Wasannin Afirka Na 2031.
  • Mulkin Kama Karya Yazo Karshe a Kasar Bulgaria

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya Najeriya
  • FIFA Na Shirin Fadada Babban Na’urar VAR A Gasar Cin Kofin Duniya 2026. Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Wasan Kwallon Kafar Najeriya A Shirye Suke Wasanni
  • Rikici Tsakanin NNPC Da Kungiyar Gwamnoni Akan Gibin Kudade Labarai
  • Oliseh, Ya Ba Eric Chelle, Shawara Da Ya Zamo Mai Tsauri AFCON 2025. Wasanni
  • Nnamdi Kanu Ya Nemi A Mayar Da Shi Abuja Daga Gidan Yarin Sokoto Labarai
  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike a Tituna Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.