Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Tayi Barazanar Zata Rage Tallafin Da Take BayarwaSudan Ta Kudu, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai

Amurka Na Zargi Kasar Rwanda Da Kokarin Saba Yarjejeniyar Zaman Lafiya
Published: December 13, 2025 at 8:03 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 13, 2025

Sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio yace take-taken kasar Rwanda a yankin gabashin kasar Kwango ta Kinshasa sun keta yarjejeniyar zaman lafiyar da aka rattaba ma hannu karkashin jagorancin shugaba Donald Trump na Amurka a Washington.

A cikin wata sanarwar da ya buga a shafin zumunci na X ranar asabar, Rubio yace a bayyane yake cewa take-taken Rwanda a gabashin Kwango sun keta yarjejeniyar zaman lafiyar, kuma Amurka zata dauki matakan tabbatar da cewa an cika alkawuran da aka yi ma shugaban Amurka.

Ranar jumma’a a zauren MDD, Amurka ta zargi kasar Rwanda da laifin rura wutar yaki da tashin hankali a saboda hare-haren da ‘yan tawayen kungiyar M23 da take marawa baya suke ci gaba da kaiwa, wadanda kuma ke neman gurgunta yunkurin Amurka na wanzar da zaman lafiya a yankin.

A ranar 4 ga watan nan na Disamba ne shugabannin Kwango Kinshasa da na Rwanda suka rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya tare da shugaba Donald Trump na Amurka a birnin Washington DC.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Kungiyar ISIS Ta Kashe Sojojin Amurka Biyu

Karin Labarai Masu Alaka

Sojojin Amurka Sun Kashe Wasu Fararen Hula Ba Dalili Amurka
Kungiyar ISIS Ta Kashe Sojojin Amurka Biyu Amurka
Trump: Zamu Kawo Zaman Lafiya A Fadin Duniya Amurka
Akwai Bukatar Bincikar Umurnin Da Sakataren Tsaro Pete Ya Bada Amurka
Amurka Ta Daina Bawa Israila Bayanan Sirri Amurka
Amurka Ta Kama Wani Jirgin Dakon Mai Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Amurka Na Zargi Kasar Rwanda Da Kokarin Saba Yarjejeniyar Zaman Lafiya
  • Kungiyar ISIS Ta Kashe Sojojin Amurka Biyu
  • Alhassan Yayi Nasarar Kifar Da Wurkilili A Gasar Damben Gargajiya
  • Anyi Jefe-Jefe Yayin Rangadin Messi, A Indiya
  • Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Iran Ta Kama Wani Jirgin Ruwa Shake Da Mai Labarai
  • Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Najeriya Ta Tabbatar Da Kyautata Rayuwar Mambobin ta Labarai
  • Gwamnonin Arewa “Mun Amince Da Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • “Hotuna” An Sako Daliban Makarantar St. Mary’s Su 100 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • GTA Hausa Logo
    Shirin Dare 2030 UTC Yau Juma’a 11.21.2025 Rediyo
  • Mun Kwato Kimanin Naira Biliyan 40 Na Badakala A Tsawon Shekara Daya Labarai
  • Shirin Manuniya Kashi Na Daya, Yau Juma’a 11.21.25 Shirye-Shirye
  • Kasar Belarus Zata Taffawa Jamhuriyar Nijar Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.