Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Kungiyar Kiristoci Ta Wanke Gwamnan Bauchi Daga Zargin Ta’addanci
Published: January 13, 2026 at 4:47 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 14, 2026

Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) reshen jihar Bauchi ta yi watsi da zarge-zargen da ake yi wa Gwamna Bala Mohammed da wasu daga cikin mukarrabansa na daukar nauyin ta’addanci, inda suka ce zargin babu tushe kuma yana da manufa ta siyasa.

A cikin wata sanarwa da shugaban CAN, Rev. Abraham Dimeus, da Sakataren ƙungiyar, Rev. Matthew Laslimbo suka sanya hannu, ƙungiyar ta bayyana cewa zargin ya kasance sharri ne da aka yi don ɓata sunan gwamnan da kuma jihar Bauchi.

Ƙungiyar ta kuma zargi cewa waɗannan ƙorafe-ƙorafen ɓangare ne na shirin abokan gaba na jihar don haifar da tashin hankali don amfanin siyasa.

Kungiyar CAN ta bayyana zarge-zargen a matsayin marasa tushe, da kuma ɓatanci ga martabar jihar Bauchi, inda ta lura cewa ana ɗaukarta a matsayin ɗaya daga cikin jihohin da suka fi zaman lafiya a arewacin Najeriya.

Ƙungiyar ta yi kira a yi hankali wajen gurfanar da wasu jami’an gwamnatin jihar Bauchi gaban kotu ta hannun hukumar yaki da Rashawa ta EFCC, tana gargadin cewa a kula sosai wajen gudanar da al’amarin don kada a haifar da tashin hankali.

Ta kuma jaddada cewa ƙungiyar addini ce ba ta da alaƙa da siyasa, CAN ta ce dole ta fito ta yi magana a matsayin ‘yan ƙasa da mazauna jihar.

Ga Rahoton Aliyu Bala Gerengi daga Gombe

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/01/BAUCHI-GOV.mp3
Labarai

Post navigation

Previous Post: Shugabar Hamayya A Venezuela Ta Gana Da Paparoma Leo
Next Post: Najeriya Da Dubai Zasu Karbi Bakoncin Taron Zuba Hannayen Jari

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumar Zabe A Najeriya Ta Cigaba Da Rijistar Katin Zabe Labarai
An Kusa Kawo Karshen Matsalolin Tsaro A Jihar Filato Afrika
Kamfanin Magani Na Aspen Yayi Gagarumar Asara A Cinikayya Afrika
Gwamnatin Jihar Filato Ta Sauke Hakimin Mushere Afrika
Iran Ta Rufe Sararin Samaniyar Ta Labarai
Matasa Sun Sayawa Ferfesa Pantami Fom Din Takarar Gwamnan Gombe Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasashen Amurka Da China Sun Matsawa Ghana Domin Rage Kudaden Haraji Afrika
  • Masar Ta Jibge Jiragen Yaki Marasa Matuka Afrika
  • Shugaba Yoweri Musevini Ya Zamo Shugaban Uganda Na 7 Yana Da Shekaru 81 Kuma Ya Shafe Shekaru 50 A Mulki Labarai
  • Sojin Kasar Congo Da ‘Yan Tawaye Sun Kara Shiga Yankin Uvira Labarai
  • Rashin Hanya da Asibiti Ya Jawo Asarar Rayuka A Jihar Gombe – Sarkin Gargajiya Afrika
  • Mabiya Dariqar Tijjaniyya Sunfara Gudanar Da Addu’oi Saboda Tsare Sheikh Sani Khalifa Zariya Afrika
  • China Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Kulla Yarjejeniya Afrika
  • “Yan Wasan Super Eagles Sun Karbi Alkawarin Da Gwamnati Tayi Musu AFCON 2023 Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.