Ranar talata Rasha take gargadin cewa yakin da Amurka da Isra’ila suka kaddamar kan Iran, zai haifar da abunda suke kokarin su hana, Moscow tace yakin zai zaburadda Iran da kasashen larabawa makwabtanta su nemi mallakar makaman Nukiliya.
Shugaban Amurka Donald Trump, ya ambato burin Iran na kera makaman Nukiliya zaman dalili da ya sa Amurka da Isra’ila suka kaddamar da hari kan Farisa da ya kai ga halaka shugaban addinin kasar Ayatollahi Ali Khameni, zargi da Iran ta musanta, kuma yanzu rikicin ya bazu a duk fadin gabas ta tsakiya.
Ministan harkokin wajen Rasha Sergei Lavrov, yace sakamakon wannan farmaki wasu shugabanni za su fito a Iran da za su kera makamin Nukiliya, abunda Amurka take so ta hana, domin sun lura cewa Amurka bata kai hari ga kasashe da suke da makamin Nukiliya.
Lavrov, yace zuwa yanzu, Rasha bata ga wata shaida da ta nuna Iran tana kera makaman Nukiliya ba. Isra’ila ce kadai a duk fadin gabas ta tsakiya take da makaman Nukiliya, abunda kasar Bani yahudun bata gaskanta ba, kuma bata musa ba.


