Wasu ‘yan majalisar dokokin Amurka guda biyar daga jam’iyyar Republican sun gabatar da kudiri a majalisar wakilai ta ƙasar domin tilasta wa sakataren harkokin wajen Amurka gabatar da cikakken rahoto kan matakan da ƙasar ke ɗauka wajen magance zargin tsananta wa addini da kisan gilla da ake cewa na faruwa a Najeriya.
Idan kudirin ya zama doka, ana sa ran ma’aikatun harkokin waje da baitulmali na Amurka za su kakaba takunkumi, ciki har da hana biza da kwace kadarori, kan “mutane ko ƙungiyoyin da ke da hannu a take ‘yancin addini” a Najeriya.
Wadanda aka ambata a cikin kudirin domin yi musu takunkumi sun haɗa da tsohon gwamnan Kano kuma jagoran jam’iyyar NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso, ƙungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) Miyetti Allah Kautal Hore da kuma waɗanda aka bayyana a matsayin “makiyayan Fulani masu ɗauke da makamai a Najeriya.”
Kudirin na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da muhawara kan batun tsaro da rikice-rikicen addini a Najeriya.
Har zuwa yanzu, babu wata sanarwa daga waɗanda aka ambata kan wannan mataki da aka gabatar a majalisar dokokin Amurka.


