Asusun bada lamuni na duniya IMF ya shawarci Afirka ta kudu ta fito da tsari da ka’idoji karara da gwamnati zata bi sau da kafa wajen rage basussuka da gwamnati take karba, asusun yana mai gargadin cewa hasashe kan tattalin arzikin ya fi nuna koma baya, duk da alamun da ake gani na samun ci gaba.
A cikin rahoton sa na shekara shekara, asusun IMF yace duk kayyadewar da kasar ta kafa game da lamarin bashi a shekara ta 2012, hakan bai hana gwamnatin kasar ci gaba da amsar basussuka ba. Duk da cewa kayyadewar ta taimaka gaya hakan bai hana karin bashi kan kasar cikin shekaru 15 da suka wuce.
Kasar Afirka ta kudu mai arzikin masna’antu ta nuna alamun hawa tudun mun tsira, bayan an kwashe wani zamani na abubuwan fallasa da durkushewar tattalin arziki da galibi suka auku zamanin mulkin shugaba Jacob Zuma.
Cikin muhimman matakai masu kyau game da Afirka ta kudu sun hada da cire kasar daga jerin kasashe da aka sakawa ido domin shigarda kudade da ake zargin sarsalar su, da kuma samun maki kyau gameda tattalin arzikin kasar, a karon farko cikin shekaru 20.


