Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Amurka Tayi Barazanar Zata Rage Tallafin Da Take BayarwaSudan Ta Kudu, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Bauchi: Ta Kaddamar Da Kwamitin Ma’adanai
Published: December 3, 2025 at 11:15 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 4, 2025

Gwamnatin Jihar Bauchi dake tarayyar Najeriya ta kaddamar da Kwamitin Cibiyar Koyon Harkokin Ma’adinai ta Alkaleri, Jihar Bauchi (MIABAS).

A yayin bikin kaddamarwar, Kwamishinan Harkokin Habaka Ma’adinai, Hon. Mohammed Maiwada Bello, ya yabawa hangen nesa da jagorancin Gwamnan Bala Mohammed, yana cewa cibiyar babban ginshiki ce da za ta inganta bincike, horaswa da kuma ƙwarewa a fannin ma’adinai.

Kwamishinan ya bayyana cewa MIABAS za ta taimaka wajen horar da matasa da kwararru a fannoni daban-daban kamar tono ma’adinai, sarrafawa, ƙara darajar ma’adinai da kuma kula da muhalli.

Hakan zai karfafa gina ƙwararru ‘yan gida, samar da ayyukan yi, da kuma tallafawa matasa a dukkan harkar ma’adinai.

An dora wa sabuwar kwamitin—wanda ya kunshi masana daga manyan ma’aikatu da cibiyoyi—alhakin kammala cikakken tsari na kafa MIABAS cikin watanni uku.

Kwamishinan ya bukaci mambobin su yi aiki da gaskiya da jajircewa domin gina cibiyar koyarwa da kirkire-kirkire ta ma’adinai wacce za ta amfanar da jihar nan da kasa baki ɗaya.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Za’a Dauko Messi Aro Zuwa Barcelona Deco
Next Post: CAF, Zata Ci Tarar Wasu Kasashe AFCON 2025

Karin Labarai Masu Alaka

Ga Alamu Jakuna Za Su Bace A Doron Kasa Nan Da Shekaru 5 Labarai
Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
Ghana Ta Haramta Hakar Ma’adinai A Gandunan Dajin Data Kebe, Labarai
Isra’ila Ta Dau Alwashin Kawo Karshen Falasdi Labarai
Addini Ko Kabilanci Basu Da Gurbi Cikin Ta’addanci Labarai
Yajin Aikin Ma’aikatan Lafiya Na Shafar Harkokin Jinya A Asibitoci Kiwon Lafiya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shirin Manuniya Yau Juma’a 12.12.2026
  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike A Tituna
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakoncin Wasannin Afirka Na 2031

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Sojoji Sun Murkushe ‘Yan Bindiga A Jihar Sakkwato Labarai
  • Tabbas Za’a Gudanar Da Gasar Firimiya Lig Ta Najeriya Wasanni
  • Abba Kabir: Zamu Samar da Jirage Marasa Matuka A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • “Hotuna” An Sako Daliban Makarantar St. Mary’s Su 100 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Bauchi Ta Amince Domin Inganta Kasuwancin Nama A Jihar Labarai
  • ECOWAS Da AU Sun Nuna Damuwa Kan Juyin Mulki A Guinea-Bissau Afrika
  • Gwamnatin Soji A Nijar Ta Hana Fitar Da Albarkatun Kasa Afrika
  • FIFA, Ta Tabbatar Da Ranar Mika Sunayen ‘Yan Wasa AFCON 2025. Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.