Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta sanar da shirin fara aikin gina babban rumbun samar da wutar lantarki ta hanyar hasken rana (solar minigrid) mai ƙarfin Megawatt biyu (2MW) a Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote (ADUST) da ke Wudil, a Jihar Kano.

Wannan aiki yana ɗaya daga cikin shirye-shiryen inganta wutar lantarki a manyan makarantun ƙasar nan ƙarƙashin manufar “Renewed Hope” ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Mataimakin Magatakardar jami’ar a ɓangaren yaɗa labarai, Malam Abdullahi Datti Abdullahi, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba. Sanarwar ta nuna cewa Shugaban Hukumar Makamashi ta Ƙasa (ECN), Dr. Mustapha Abdullahi, ne ya bayar da wannan labari yayin da yake karɓar baƙuncin Shugaban Jami’ar ADUST, Farfesa Musa Tukur Yakasai, a ofishinsa da ke Abuja.
An bayyana cewa Ma’aikatar Kimiyya da Fasaha ta Tarayya ta riga ta ba da kwangilar aikin akan kuɗi har naira biliyan uku da ɗigo takwas (₦3.8 billion). Ana sa ran kammala aikin cikin wata uku kacal domin fara amfanar ɗalibai da malaman makarantar.
Shugaban na ECN, wanda tsohon ɗalibin jami’ar ne, ya bayyana cewa yayin da mafi yawan jami’o’in ƙasar nan ke samun tagomashin Megawatt guda, ita ADUST za a ba ta Megawatt biyu ne saboda girma da kuma buƙatar makarantar.
Dr. Abdullahi ya ƙara da cewa:
”Wannan shiri na sanya hasken rana ba kawai a jami’o’i ya tsaya ba, ya shafi asibitoci da yankunan karkara a duk faɗin jihohin Najeriya domin rage radadin rashin wuta.”
Haka kuma, ya sanar da cewa jami’ar za ta sake samun ƙarin fitulun kan hanya (streetlights) guda 200, baya ga guda 200 da aka riga aka kafa musu a kwanakin baya.
A nasa ɓangaren, Shugaban Jami’ar ADUST, Farfesa Yakasai, ya jinjina wa Dr. Abdullahi kan yadda yake kishin tsohuwar makarantarsa. Ya bayyana cewa waɗannan ayyuka za su taimaka kwarai wajen inganta tsaro a cikin jami’ar da kuma sauƙaƙa gudanar da bincike a dakunan gwaje-gwaje (laboratories).
Farfesa Yakasai ya kuma yaba wa Shugaban na ECN kan gudunmawar da ya bayar wajen karɓar baƙuncin wasannin share-fage na NUGA na shekarar 2025 da jami’ar ta yi. Daga nan sai ya buƙaci ƙarin haɗin gwiwa wajen kafa babban dakin binciken makamashi (energy laboratory) a jami’ar.
Wannan aiki na zuwa ne daidai lokacin da Gwamnatin Tarayya ta ƙara kaimi wajen samar da madadin wutar lantarki ga manyan cibiyoyi, inda kwanan nan aka ƙaddamar da makamancinsa mai ƙarfin Megawatt 7.1 a Jami’ar Bayero ta Kano (BUK).


