Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Amurka Tayi Barazanar Zata Rage Tallafin Da Take BayarwaSudan Ta Kudu, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Jihohin Arewaci Sun Kafa Asusun Yaki Da Ta’addanci
Published: December 1, 2025 at 8:24 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Gwamnonin Arewacin Najeriya, sun kaddamar da Asusun tsaro a yankin, Inda kowacce jiha za ta ba da Biliyan ɗaya duk wata.

Gwamnonin jihohin Arewacin Najeriya tare da sarakunan gargajiya sun sanar da kafa Asusun tsaro na yankin Arewa, wanda kowace jiha da kananan hukumomin ta za su riƙa ba da naira biliyan ɗaya a duk wata domin magance matsanancin tsaro a yankin.

Sanarwa mai dauke da sa hannun Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya, Gwamnan jihar Gombe, kuma shugaban kungiyar Gwamnonin Arewa ta bayyana cewa, wannan na cikin muhimman matsaloli da aka cimma a ƙarshen taron haɗin gwiwar Kungiyar Gwamnonin Arewa da Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Arewacin Najeriya, da aka gudanar a ranar Litinin a gidan Sir Kashim Ibrahim dake Kaduna.

Taron ya samu halartar dukkan gwamnonin jihohin Arewa guda goma sha tara (19) da shugabannin majalisun gargajiya na kowacce jiha.

A yayin taron an tattauna kan manyan batutuwa da suka shafi yankin da Najeriya baki ɗaya, inda aka yanke waɗannan muhimman shawarwari.

Gaisuwar ta’aziyya ga jihohin da hare hare suka shafa. Gwamnonin sun yi jaje ga gwamnatoci da al’ummomin Kebbi, Kwara, Kogi, Neja, Sakkwato, Jigawa da Kano bisa kashe-kashe da sace sacen ‘yan makaranta da al’umma da aka yi a kwanakin baya haka kuma an miƙa ta’aziyya ga waɗanda hare-haren Boko Haram suka rutsa da su a Borno da Yobe.

Dakatar da hakar ma’adanai na wucin gadi:

Gwamnonin sun nuna damuwa kan yadda hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba ke kara haifar da matsalolin tsaro a Arewacin kasar a saboda haka sun bukaci shugaban ƙasa ya umarci Ministan Ma’adanai ya dakatar da dukkan hakar ma’adanai na watanni shida, domin gudanar da cikakken bincike da tantance lasisin hako ma’adanai tare da hadin gwiwar gwamnonin jihohi.

Kafa Asusun Tsaro na Yanki:

A wani muhimmin mataki, kungiyar ta amince da kafa asusun tsaro na Yankin Arewa, wanda za a rika ba da naira biliyan ɗaya daga kowace jiha da kananan hukumomi duk wata, domin sauƙaƙa yaki da kalubalen tsaro.

Sannan tattaunawar ta amince a sake gudanar da wani taro a wani lokaci da za a sanar nan gaba.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Gwamnonin Arewa “Mun Amince Da Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi”
Next Post: Matatar Man Dangote Zata Wadatar Da Najeriya Da Makota

Karin Labarai Masu Alaka

An Kashe Mutum 2 Da Suka Ba ‘Yan-Matan (GGCSS Maga) Kariya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaba Tinubu Ya Umurci Janyewa Manyan Mutane ‘Yan Sanda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Ya Zamo Khalifan Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan-Ta’adda Sun Kara Sace Mutane A Jihar Naija! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan Kungiyar Boko Haram Sun Yi Awon Gaba Da Mata 13 A Borno Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sunayen Jakadu: Kungiyar CISLAC Ta Nemi A Janye Sunan Mr. Ayodele Oke Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike a Tituna
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakuncin Wasannin Afirka Na 2031.
  • Mulkin Kama Karya Yazo Karshe a Kasar Bulgaria

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Tsohon Minista Ngige Ya Shiga Komar EFCC Najeriya
  • Musa: “Da Yaddar Allah Zamu Ga Bayan Ta’addanci A Najeriya” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • FIFA Na Shirin Fadada Babban Na’urar VAR A Gasar Cin Kofin Duniya 2026. Wasanni
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Talata 11.18.2025 Rediyo
  • Abun Da Kuke Buƙatar Sani Game Da Gasar Cin Kofin Ƙasashen Afirka 2025 Wasanni
  • Gwamnatin Kano: Zamu Kara Daukar Malamai Domin Inganta Ilimi Najeriya
  • Okoye Na Shirin Maye Gurbin Nwabali, AFCON 2025: Wasanni
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.