Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Jihohin Arewaci Sun Kafa Asusun Yaki Da Ta’addanci
Published: December 1, 2025 at 8:24 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Gwamnonin Arewacin Najeriya, sun kaddamar da Asusun tsaro a yankin, Inda kowacce jiha za ta ba da Biliyan ɗaya duk wata.

Gwamnonin jihohin Arewacin Najeriya tare da sarakunan gargajiya sun sanar da kafa Asusun tsaro na yankin Arewa, wanda kowace jiha da kananan hukumomin ta za su riƙa ba da naira biliyan ɗaya a duk wata domin magance matsanancin tsaro a yankin.

Sanarwa mai dauke da sa hannun Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya, Gwamnan jihar Gombe, kuma shugaban kungiyar Gwamnonin Arewa ta bayyana cewa, wannan na cikin muhimman matsaloli da aka cimma a ƙarshen taron haɗin gwiwar Kungiyar Gwamnonin Arewa da Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Arewacin Najeriya, da aka gudanar a ranar Litinin a gidan Sir Kashim Ibrahim dake Kaduna.

Taron ya samu halartar dukkan gwamnonin jihohin Arewa guda goma sha tara (19) da shugabannin majalisun gargajiya na kowacce jiha.

A yayin taron an tattauna kan manyan batutuwa da suka shafi yankin da Najeriya baki ɗaya, inda aka yanke waɗannan muhimman shawarwari.

Gaisuwar ta’aziyya ga jihohin da hare hare suka shafa. Gwamnonin sun yi jaje ga gwamnatoci da al’ummomin Kebbi, Kwara, Kogi, Neja, Sakkwato, Jigawa da Kano bisa kashe-kashe da sace sacen ‘yan makaranta da al’umma da aka yi a kwanakin baya haka kuma an miƙa ta’aziyya ga waɗanda hare-haren Boko Haram suka rutsa da su a Borno da Yobe.

Dakatar da hakar ma’adanai na wucin gadi:

Gwamnonin sun nuna damuwa kan yadda hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba ke kara haifar da matsalolin tsaro a Arewacin kasar a saboda haka sun bukaci shugaban ƙasa ya umarci Ministan Ma’adanai ya dakatar da dukkan hakar ma’adanai na watanni shida, domin gudanar da cikakken bincike da tantance lasisin hako ma’adanai tare da hadin gwiwar gwamnonin jihohi.

Kafa Asusun Tsaro na Yanki:

A wani muhimmin mataki, kungiyar ta amince da kafa asusun tsaro na Yankin Arewa, wanda za a rika ba da naira biliyan ɗaya daga kowace jiha da kananan hukumomi duk wata, domin sauƙaƙa yaki da kalubalen tsaro.

Sannan tattaunawar ta amince a sake gudanar da wani taro a wani lokaci da za a sanar nan gaba.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Gwamnonin Arewa “Mun Amince Da Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi”
Next Post: Matatar Man Dangote Zata Wadatar Da Najeriya Da Makota

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Tinubu Ya Kara Aika Sunayen Jakadu Ga Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Tinubu: Zamu Kara Kyautata Samar Da Kayan Aiki Ga Jami’an Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Fara Azumin Watan Ramadan A Najeriya Da Sassan Duniya  Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Tinubu: Abba Magajin Aminu Kano Ne A Fagen Siyasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Guinea Bissau Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar HPV A Jihar Gombe Ta Jagoranci Yaki Da Karuwar Cutar Daji
  • Majalisar Dokokin Kamaru Ta Amince Da Wasu Sauye Sauye
  • Jami’an Tsaro Suna Farautar Wasu ‘Yan Ta’adda A Najeriya
  • Rasha Takai Hari Ukraine Da Jirgi Marar Matuki
  • Isra’ila Zata Kai Hari Cibiyar Makamashin Iran

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Man Da Matatar Dangote Take Fitarwa Zuwa Kasashen Afirka Ya Karu Afrika
  • Rundunar Sojin Iran Tace Harin Amurka Ya Kashe Musu Sama Da Mutane Dari Afrika
  • Farashin Dalar Amurka Ya Tashi Ranan Juma’a Amurka
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Turkiyya Ta Zargi Alakar Isra’ila Da Somaliya Afrika
  • Jirgin Sama Ya Fadi A Kano Labarai
  • ‘Yan Kungiyar Boko Haram Sun Yi Awon Gaba Da Mata 13 A Borno Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hukumar MDD Tace Wadanda Suka Mutu A Harin Sudan Sun Haura 70 Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.