Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kyautata Dangantaka Tsakanin Jami’an Tsaro Da Al’umma Ce Mafita
Published: November 22, 2025 at 3:30 AM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: November 23, 2025

Masana harkokin tsaro a Najeriya sun bayyana cewa kyakkyawar alaka da fahinta tsakanin jami’an tsaro da al’umma, suna da gagarumin tasiri wajen magance matsalolin tsaro da samun zaman lafiya mai dorewa.
A wata tattaunawa ta musamman da sashen hulda tsakanin farar hula da jami’an soji da shelkwatar rundunar ta shirya da manema labarai a Jos, jihar Filato, masana harkokin tsaro, jami’an soji da ‘yan jarida sun dauki wuni guda suna fadakar da juna matakan da kowa zai bi wajen samadda masalaha kan matsalolin tsaro da suka addabi Najeriya.
Birgediya Janar Sani Usman Kukasheka mai ritaya, wanda ya gabatar da kasida mai taken “Tasirin Fasahar dake tasowa kan kafafen watsa labarai da hadin gwiwa tsakanin soji da kafafen watsa labarai”, ya bayyana cewa idan har ‘yan jarida sun fahinci yadda soja ke gudanar da aikinsu, suka kuma fadakar da al’umma, ba shakka za’a sami ci gaba.
Madam Ayuku Pwaspo, shugabar kungiyar ‘yan Jarida ta kasa reshen jihar Filato, ta bukaci manema labarai su gudanar da aikinsu bisa ka’ida don hadin kan kasa.
Shugaban sashen hulda tsakanin farar hula da soji, Manjo Janar Musa Etsu-Ndagi yace ‘yan jarida na da gagarumin gudunmawar fadakar da jama’a yadda soja ke aiki.
Hajiya Hadiza Hassan, ‘yar jarida dake aiki a gidan Rediyo da Talabijin na Unity a Jos, tace ta karu sosai daga tattaunawar.
Wassu faifan bidiyo da hotuna da rundunar sojin da nuna sun bayyana irin tallafi da sojoji ke baiwa al’umma da suka hada da gyara da gina makarantu da asibitoci, tallafin kayan abinci ga wadanda suka shiga ibtila’i da sauransu.
Najeriya

Post navigation

Previous Post: Manya-Manyan Wasannin Wannan Makon
Next Post: Tsananta Hukunci Ga Masu Fyade Kan Takaita Cin Zarafin Yara

Karin Labarai Masu Alaka

Najeriya Tayi Asarar Kusan Naira Triliyan 1 Sakamakon Harajin Trump Amurka
Malami: Gwamnatin APC Ta Gaza – “Yan-Kasa Kuwa Na Da Katin Zabe” Labarai
Mutane Biyu Sun Rasa Rayukansu A Hatsarin Da Ya Rutsa Da Antothy Joshua Najeriya
Tinubu Ya Nada Shugabannin Hukumar NERC Najeriya
Hukumar CAC Zata Dakatar da POS Mara Rijista a Kasar Najeriya
Akwai Alamar Shawarwari Tsakanin Amurka Da Turai Zai Kawo Karshen Yakin Rasha Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • An Gano Wasu Boma Bomai Da Aka Binne A Jihar Neja Najeriya
  • Umar Aliyu, Shugaban Magoya Bayan Wikki Tourist
    Jagorancin Wikki Tourist FC Na Samun Yabo Wasanni
  • Adamu: “Yakar Cin Hanci Daga Tushe Itace Mafita Daya Tilo” Labarai
  • Mace Ta Farko Da Zata Shugabanci Jami’ar Northwest Dake Kano Najeriya
  • Nigeria Zata Bude Asusun Dala Bilyan Biyu Don Habaka Sashin Makamashi Labarai
  • Wani Dan Bindiga Ya Harbi Dakarun Tsaron Cikin Gida Su Biyu A Washington DC Labarai
  • Yau Lahadi Ake Gudanar Da Zabe A Kasar Myanmar Labarai
  • Tinubu: Sojojin Mu Sun Yi Rawar Gani Don Kare Demokuraɗiyya A Jamhuriyar Binin Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.