Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Amurka Tayi Barazanar Zata Rage Tallafin Da Take BayarwaSudan Ta Kudu, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Masana: ‘Yancin Kasashen Afrika A Rubuce Yake Ba A Zahirance Ba
Published: December 7, 2025 at 5:16 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Tun fiye da shekaru sittin da mafi yawan kasashen Afirka suka sami ‘yancin kai, masana sun bayyana cewa har yanzu nahiyar na fama da tsarin mulkin mallaka da rashin samun ‘yanci a fannoni daban-daban na rayuwa.
A wani taro da masana daga kasashen duniya suka halarta, da masu fafutukar ‘yanci da hukumomi da dalibai daga kasashe daban-daban na Afirka, wadanda suka taru a Jami’ar Jos, an gabatar da kasidu da suka yi nazari kan makomar Nahiyar Afirka da hanyoyin samar da mafita.
Taron na tunawa da wani matubuci da fafutuka, Frantz Fanon da yayi rubuce-rubuce da suka zame kamar wahayi kan makomar nahiyar Afirka a fannonin damokradiyya, gazawar shugabanci da sauransu.
Malam Jibrin Ibrahim na cibiyar damokradiyya da ci gaba dake Abuja, Najeriya, yace taron yayi nazari ne kan rashin tasiri da ‘yancin kai a Afirka ya kasance.
Shima Malam Yunusa Zakari-Ya’u na cibiyar fasahar sadarwa da ci gaba dake Kano, Najeriya, yace yawan juyin mulki da ake samu a wassu kasahen Afirka, saboda rashin adalcin shugabanni ne.
Komared Sam Magaji, malami a Jami’ar Jos, yace suna horadda dalibai su san yadda shugabanni a baya suka yi mulki, da yadda daliban zasu yi nazarin abubuwan dake faruwa yanzu, da yadda za’a yi gyara nan gaba.
Mr Charles Toheyo, malami a Jami’ar Nkerere dake kasar Uganda, yace idan har shugabannan dake mulki basu sauya tunaninsu ta yadda zasu kyautata wa al’umma ba, to ba shakka za’a ci gaba da zaman tankiya.
Adam Khalid, dalibi a Jami’ar Jos, yace matasa a Afirka a shirye suke su kawo sauyi, sai dai har yanzu basu sami jagoranci daga dattawa ba, saboda dattawan kansu kadai suka sani.
A taron na wuni biyu, an gabatar da kasidu kimanin saba’in, da suka kunshi samarda mafita kan matsalolin da suka hana kasashen Afirka samun walwala da ci gaba.
https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/12/DAMOKRADIYYA-A-AFIRKA.mp3
Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Bauchi: Ba Zamu Bude Makarantu Ba Sai 2026
Next Post: Marc Brys: “Eto’o Baiyi Adalci Ga Onana, Da Vincent, Ba”

Karin Labarai Masu Alaka

Akwai Bukatar Hukunci Mai Tsanani Ga Duk Wanda Yayi Fyade Najeriya
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Tsohon Minista Ngige Ya Shiga Komar EFCC Najeriya
Sunayen Jakadu: Kungiyar CISLAC Ta Nemi A Janye Sunan Mr. Ayodele Oke Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Eziekel Gomos Ya Zamo Babban Daraktan Sakatariyar Zauren Gwamnonin Arewa Najeriya
Jakadan Kasar Sin a Najeriya Ya Ziyarci Tinubu Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shirin Manuniya Yau Juma’a 12.12.2026
  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike A Tituna
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakoncin Wasannin Afirka Na 2031

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Litinin 11.17.2025 Rediyo
  • Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan-Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Daliban St. Mary! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ga Alamu Jakuna Za Su Bace A Doron Kasa Nan Da Shekaru 5 Labarai
  • Ukraine Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Tsarin Cimma Yarjejeniya Sauran Duniya
  • Gasar Cin Kofin Nahiyar Afrika A Wannan Makon Wasanni
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Juma’a 11.21.2025 Rediyo
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.