Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Najeriya Da Dubai Zasu Karbi Bakoncin Taron Zuba Hannayen Jari
Published: January 13, 2026 at 4:58 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 13, 2026

Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya sanar da cewa Najeriya za ta karɓi bakuncin taron Investopia tare da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE) a birnin Legas a watan Fabrairu mai zuwa, domin jawo hankalin masu zuba jari daga sassa daban-daban na duniya.

Shugaban ƙasar ya bayyana hakan ne a yayin taron Abu Dhabi Sustainability Week (ADSW) na shekarar 2026, inda ya ce shirin zai taimaka wajen bunƙasa jarin da zai tallafa wa ci gaban tattalin arziki mai dorewa.

A gefen taron, Najeriya da UAE sun kuma rattaba hannu kan yarjejeniyar tattalin arziki ta CEPA, wadda ke da nufin zurfafa haɗin gwiwa a fannonin kasuwanci, makamashi, gine-gine, sufurin kayayyaki da kasuwancin zamani na intanet.

Shugaban UAE, Sheikh Mohamed bin Zayed Al Nahyan, tare da ministocin kasashen biyu, sun halarci sanya hannun kan yarjejeniyar da Tinubu ya bayyana a matsayin tarihi da dabarar bunkasa dangantakar kasashen biyu.

Tinubu ya bayyana cewa Investopia zai haɗa masu zuba jari, ‘yan kasuwa, masu kirkire-kirkire da masu tsara manufofi domin mayar da ra’ayoyi zuwa jarin da zai amfani al’umma, sannan ya ce Najeriya na da burin tara kusan dala biliyan 30 a duk shekara domin ayyukan sauyin yanayi da masana’antu masu kare muhalli, yana mai jaddada bukatar sauya tsarin hada-hadar kuɗin duniya domin sauƙaƙa wa ƙasashe masu tasowa samun jari ba tare da nauyin bashi ba.

Shugaban ƙasar ya kuma yi nuni da gyare-gyaren makamashi da tattalin arziki da gwamnatinsa ke aiwatarwa, ciki har da Dokar Lantarki ta 2023 da kuma manufofin kasuwar carbon, yana cewa hakan ya ƙara amincewar masu zuba jari.

Ya ƙara da cewa fitar da kayayyakin da ba na mai ba ya ƙaru da kashi 21 cikin 100, tare da alkawarin cewa Najeriya a shirye take ta yi aiki da abokan hulɗa domin gina ci gaba mai ɗorewa, adalci da amfani ga kowa.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Kungiyar Kiristoci Ta Wanke Gwamnan Bauchi Daga Zargin Ta’addanci
Next Post: Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo

Karin Labarai Masu Alaka

Mutane Biyu Sun Rasa Rayukansu A Hatsarin Da Ya Rutsa Da Antothy Joshua Najeriya
CAN: Da Alamu Daliban St. Mery Na Cikin Koshin Lafiya Najeriya
Kyautata Dangantaka Tsakanin Jami’an Tsaro Da Al’umma Ce Mafita Najeriya
Akwai Alamar Shawarwari Tsakanin Amurka Da Turai Zai Kawo Karshen Yakin Rasha Amurka
Najeriya Tayi Asarar Kusan Naira Triliyan 1 Sakamakon Harajin Trump Amurka
Tinubu: Ku Guji Yi Wadaka Da Kudin Kananan Hukumomi Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • NLC Ta Yabawa Gwamnan Gombe Inuwa Yahaya Najeriya
  • Gwamnatin Gombe Zata Inganta Samar Da Wuta Wajen Amfani Da Hasken Rana Kimiya
  • Abu Mafi Daukar Hankali A Wasan Dambe Na Yau Wasanni
  • Shugaba Trump Yace Amurka Ce Zata Rika Gudanar Da Harkokin Kasar Venezuela Amurka
  • Akwai Yiwuwar Shugaban Ƙasar Afirka Ta Tsakiya Touadera Yasamu Nasara A Karo Na Uku Afrika
  • Kudi Sunfi Rayuwar Mutum Muhimmanci A Asibitocin Najeriya Kiwon Lafiya
  • Hukumar Hisbah Ta Kona Barasar Dubban Nairori A Katsina Labarai
  • Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Zuwa Jami’ar Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.