Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Amurka Tayi Barazanar Zata Rage Tallafin Da Take BayarwaSudan Ta Kudu, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Nijar: Zamu Tsananta Bincike A Bakin Iyakokin Mu
Published: December 9, 2025 at 6:51 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: December 9, 2025

Hukumomi a jamhuriyar Nijar sun umurci jami’an fiton kaya (Douanes) da su tsaurara binciken kayan da ke shigowa kasar daga Najeriya. Matakin wanda ke da nasaba da dalilan tsaro, wanda a ‘yan kwanaki kadan da suka shige aka samu tarin wasu ababe masu fashewa a wata motar jigila da ta tsallaka Nijar daga wata kasar waje. Tuni ‘yan kasuwa da kungiyoyin fararen hula suka fara bayyana matsayinsu a kai.

Ta hanyar wata takardar da ya aike wa mukarrabansa na illahrin jihohi ne shugaban hukumar Douanes na kasa Kanal Mohamed Yacouba Siddo ya umurce su da kara zuba ido kan kayayakin da ke shiga Nijar ta iyakar ta da Najeriya, abinda ke nufin daga yanzu za a sauke kayayakin da matakin ya shafa domin yi masu dai dai kafin samun izinin tsallakowa Nijar.

Shugaban kungiyar ‘yan kasuwar Import Export Alhaji Yacouba Dan Maradi ya ce, matakin wanda a ka ayyana cewa abu ne da ke da nasaba da harakokin tsaro na zuwa ne a wani lokacin da alamu ke nuna yadda barazanar tsaro ke kara fadada a kasashen sahel da na yammacin Afirka, A ra’ayin shugaban kungiyar ci gaban karkara da birane Alhaji Ali Kalla matakin ya zo a kan gaba.

Koda yake a na danganta abin da yanayin tsaro wasu daga cikin mazauna garuruwan iyakar kasashen biyu na da fargaba game da yadda za a tafiyar da shi.

Iyakar Nijar da Najeriya mai tsawon kilo mita sama da 1500 na matsayin iyaka mafi mahimmanci ga kowacce daga cikinsu, kasancewarta gimshiki a harakokin tattalin arziki da cudanyar al’umomin kasashen biyu. jihohi a kalla 5 na Nijar ne ke makwaftaka da jihohi 7 na arewacin Najeriya.

TSAURARA BINCIKE A IYAKAR NIJAR NAJERIYA

 

Afrika

Post navigation

Previous Post: Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro
Next Post: Eziekel Gomos Ya Zamo Babban Daraktan Sakatariyar Zauren Gwamnonin Arewa

Karin Labarai Masu Alaka

Muna Kira Ga Kasashen Duniya Su Sa Baki Don A Saki Mohamed Bazoum Afrika
Najeriya: Ba Don Leken Asiri Muka Tura Jirgin Yakin Mu Ba Afrika
Amurka Ta Gabatarwa Sassan Dake Yakar Juna A Sudan da Shirin Tsagaita Wuta Afrika
Kasar Congo Ta Dau Alwashin Bin Tsari Wajen Rarraba Ma’adanai Afrika
ECOWAS Da AU Sun Nuna Damuwa Kan Juyin Mulki A Guinea-Bissau Afrika
Gwamnatin Kasar Benin Ta Nemi ‘Yan Kasa Su Kwantar Da Hankali Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike a Tituna
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakuncin Wasannin Afirka Na 2031.
  • Mulkin Kama Karya Yazo Karshe a Kasar Bulgaria

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Nnamdi Kanu Ya Nemi A Mayar Da Shi Abuja Daga Gidan Yarin Sokoto Labarai
  • Amurka Zata Saidawa Saudiyya Da Jirgin Yaki Samfurin F35 Labarai
  • Gwamna Zulum: Ya Bukaci Sojoji Su Cigaba Da Yakar Boko Haram Da ISWAP Labarai
  • Janet Ce Gwarzuwar ‘Yar Wasan Mako NWFL Wasanni
  • FIFA, Ta Tabbatar Da Ranar Mika Sunayen ‘Yan Wasa AFCON 2025. Wasanni
  • Gwamnatin Jihar Kano Zata Kashe Makudan Kudade Ga Jama’ar Kano! Najeriya
  • Oliseh, Ya Ba Eric Chelle, Shawara Da Ya Zamo Mai Tsauri AFCON 2025. Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.