Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Tayi Barazanar Rage Tallafinta Wa Sudan Ta Kudu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai

Sojojin Kasar Isra’ila Sun Kashe Wani Babban Kwamandan Hamas
Published: December 14, 2025 at 6:17 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar sojojin bani Isra’ila ta ce ta kashe wani babban kwamandan Hamas mai suna Raed Saed, a harin da ta kai kan wata mota ranar asabar a birnin Gaza.

Wannan shine kisa na wani babban dan kungiyar Hamas na farko tun lokacin da aka kulla yarjejeniyar tsagaita wuta a watan Oktoba.

A wata sanarwar hadin guiwa, firaminista Benjamin Netanyahu da ministan tsaron kasar sunce an kai hari a kan Saed ne a bayan wani harin da Hamas ta kai da nakiya ta raunata wasu sojojin Isra’ila biyu ranar asabar.

Hukumomin kiwon lafiya a Gaza sun ce harin da Isra’ila ta kai kan motar a birnin gaza ya kashe mutane biyar, ya raunata wasu akalla 25. Amma ba a ji daga bakin kungiyar Hamas ko ma’aikatan kiwon lafiya a kan ko akwai Saed a cikin wadanda aka kashe ba ya zuwa yanzu.

A cikin wata sanarwar da ta bayar, hamas tayi Allah wadarai da wannan harin a zaman wanda ya keta yarjejeniyar tsagaita wuta, amma ba ta tabbatar da ko akwai Saed a cikin wadanda aka kashe ba, haka kuma ba ta yi barazanar daukar fansa ba.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Tattalin Arzikin Kasar Bahrain Ya Bunkasa Sakamakon Ruruwar Masu Yawon Bude Ido
Next Post: Sojoji Sun Farmaki ‘Yan Ta’adda A Borno

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Bauchi: Ta Kaddamar Da Kwamitin Ma’adanai Labarai
Nuhu Ribadu Ya Mika Dalibai 100 da Aka Ceto Ga Gwamnatin Jihar Neja Labarai
Akwai Bukatar Bin Dokokin Tuki A Kan Hanyoyi Labarai
Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
Mun Kwato Kimanin Naira Biliyan 40 Na Badakala A Tsawon Shekara Daya Labarai
Wasan Hamayya (Istanbul Derby) Fenerbahçe Da Galatasaray 1-1 Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • NLC Ta Yabawa Gwamnan Gombe Inuwa Yahaya
  • Jirgin Sama Ya Fadi A Kano
  • Shugaba Tinubu Ya Yayi Magana Game Da Kafa ‘Yan Sandan Jihohi
  • Tinubu Yafara Wasu Dabaru Domin Samun Kuri’u
  • Sojoji Sun Farmaki ‘Yan Ta’adda A Borno

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Ya Zamo Khalifan Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Allah Ya Yi Wa Sheikh Dahiru Bauchi Rasuwa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Kano: Zamu Kara Daukar Malamai Domin Inganta Ilimi Najeriya
  • Akwai Bukatar Hukunci Mai Tsanani Ga Duk Wanda Yayi Fyade Najeriya
  • ECOWAS Zata Taimakawa Kasar Benin Da Dakarun Soji Afrika
  • Ministan Tsaron Najeriya Badaru Yayi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan-Ta’adda Sun Kara Sace Mutane A Jihar Naija! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Asabar 11.22.2025 Rediyo
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.