Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Wasan Dambe Ya Dau Sabon Salo A Jihar Inugu
Published: December 19, 2025 at 2:56 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Al’ummar Arewa a Jihar Inugu na ci gaba da yin sam-barka tare da bayyana farin ciki da bude sabon gidan damben gargajiya da aka yi a Inugu babban birnin jihar bayan shafe shekaru da wasan ya dauke.

Mai gidan damben Cif Emeka Nnolim, wani dan kabilar Igbo ya ce, “Wannan hanya ce ta hada kawunan kabilu daban-daban na Najeriya don karfafa zumunci ta hanyar raya wasan dambe a tsakanin matasan Arewa da ke wannan jihar da wadanda suke nesa. Wannan matakin farko ne na bunkasa wasannin gargajiya a Jihar Inugu don mayar da jihar cibiyar wasannin gargajiya a Najeriya.”

Bayan kammala bude filin wasan, shugaban al’ummar Arewa a jihar da kuma babban mai taimaka wa gwamnan Jihar Inugu kan ayyuka na musamman, Alhaji Abubakar Yusuf Sambo ya tofa albarkacin bakinsa kan dawowar wasan dambe a jihar.

“Na yi farin ciki da ganin cewa da duk da cewa muna kudancin Najeriya muna tuna abin da aka san Arewa da shi watau wasan dambe. Wasa ne na hada zumunci, kuma duk inda ake irin wannan zamu bada goyon baya,” inji Alhaji Yusuf Sambo.

A cewar wani dan dambe dan asalin garin Hadejia na Jihar Jigawa mai suna Adamu wanda aka fi sani da Shagon Baturiya, “Wasa ya yi dadi yadda ake so. Sabon gidan dambe da aka bude anan Inugu ya yi kyau. Na yi farin ciki kuwa,” a yayin da wani shahararren dan wasa Badaman Bauchi, shi ma cike da farin ciki, ya mika goron gayyata zuwa daukacin ‘yan wasa da cewa:

“Filin sabon gidan wasan dambe da aka bude a Inugu ba laifi. Toh domin haka, muna kira ga sauran ‘yan wasa da suke nesa da su zo. Muna gayyatar kowa da kowa su zo.”

An bude gidan damben ne unguwar Emene wacce take cikin birnin Inugun, inda matasan Arewa sun fara tururuwa don nishadantar da kansu da take taken ‘yan wasa da kide-kiden gargajiya masu faranta ran gaske.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Sanda Sunce Mutum Daya Ne Yakai Hare-Haren Jami’ar Brown Da Kuma Na MIT Boston
Next Post: Shugaba Tinubu Ya Gabatar da Kasafin Kuɗin 2026

Karin Labarai Masu Alaka

CAF, Zata Ci Tarar Wasu Kasashe AFCON 2025 Wasanni
Marc Brys: “Eto’o Baiyi Adalci Ga Onana, Da Vincent, Ba” Wasanni
Senegal Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirka Afcon 2025. Wasanni
Kungiyar Enyimba: Bamu Da Niyyar Rage Albashin ‘Yan-Wasa Wasanni
Liverpool Tayi Rashin Nasara A Wasanni Tara Wasanni
Kungiyar Kwallon Mata Sun Tsallaka Iyakar Turkiyya Zuwa Iran Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Talata 11.18.2025 Rediyo
  • Kungiyar Kiristoci Ta Wanke Gwamnan Bauchi Daga Zargin Ta’addanci Labarai
  • Gwamnatin Amurka Na Kokarin Watsi Da Tsohuwar Dokar Jones Labarai
  • An Tsinto Gawarwakin ‘Yan gudun Hijira A Bakin Tekun Comoros Labarai
  • Ana Cigaba Da Samun Hare Hare Da Jiragen Marasa Matuki A Sudan Labarai
  • Sanarwar MDD Ya Nuna Aniyar Mayakan RSF Na Kisan Kare Dangi Afrika
  • Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal Ya Bar PDP Ya Koma APC Labarai
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.