Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Real Madrid: Ta Kori Xabi Alonso Bayan Rashin Nasara A Wasan Kofin Sfaniya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
Published: January 14, 2026 at 8:05 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayyar Najeriya da ASUU sun kulla yarjejeniya ta farko a tarihi domin kawo karshen yawan yajin aiki a jami’o’in Najeriya

A wani muhimmin mataki da ake ganin zai sauya fasalin ilimin jami’a a Najeriya, Gwamnatin Tarayya da Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Ƙasa (ASUU) sun kulla wata babbar yarjejeniya da nufin inganta jin daɗin malamai, tabbatar da zaman lafiyar aiki da kuma kawo ƙarshen yawan yajin aikin da ya shafe shekaru yana durƙusar da jami’o’in ƙasar.

An bayyana yarjejeniyar ta shekarar 2025 tsakanin Gwamnatin Tarayya da ASUU a ranar Laraba a Abuja, inda Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa, ya bayyana ta a matsayin wani sabon shafi a tarihin ilimin gaba da sakandare a Najeriya.

A cewarsa, yarjejeniyar ba rubutun takarda bane kawai, illa alamar dawo da amana, girmamawa da kwarin gwiwa ga tsarin jami’o’in ƙasar bayan shekaru na rashin tabbas da yajin aiki.

Ministan ya yabawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa daukar mataki na musamman wajen fuskantar matsalar da ta dade tana addabar jami’o’i, tana lalata jadawalin karatu tare da rusa makomar dalibai miliyoyi.

“Wannan ne karon farko da Shugaban Ƙasa mai ci ya tsaya tsayin daka wajen fuskantar wannan ƙalubale kai tsaye, ya ba matsalar kulawar shugabancin da ta dace,” in ji Alausa, yana mai cewa gwamnatin ta zaɓi tattaunawa maimakon rikici, gyara maimakon jinkiri, da warware matsala maimakon surutu.

Daya daga cikin manyan abubuwan da yarjejeniyar ta ƙunsa shi ne ƙarin albashin malaman jami’a da kashi 40 cikin 100, wanda Hukumar Albashi, Kuɗaɗen Shiga da Albashi ta Ƙasa (NSIWC) ta amince da shi Sabon tsarin albashin zai fara aiki daga ranar 1 ga Janairu, 2026.

A karkashin sabon tsarin, albashin malaman zai haɗa da CONUASS da kuma ingantaccen alawus na kayan aikin koyarwa da bincike (CATA). An ƙarfafa CATA domin tallafa wa wallafa mujallu, halartar taruka, amfani da intanet, rajistar ƙungiyoyin ƙwararru da rubuce-rubucen littattafai, domin ƙara gogayya da rage guduwar ƙwararru zuwa ƙasashen waje.

Haka kuma, yarjejeniyar ta sake tsara alawus-alawus guda tara na Earned Academic Allowances, inda aka fayyace su sarai tare da danganta su kai tsaye da ayyukan da ake yi kamar kula da daliban digirin digirgir, aikin asibiti, jarrabawa da shugabancin harkokin ilimi.

A wani sabon salo da ba a taba gani ba a tsarin jami’o’in Najeriya, Gwamnatin Tarayya ta amince da wani alawus na musamman ga manyan malaman jami’a, wato Farfesoshi da Masu Karatu (Readers).

A karkashin wannan tsari, Farfesoshi za su rika karɓar naira miliyan 1.74 a shekara (naira 140,000 a wata), yayin da Readers za su karɓi naira 840,000 a shekara (naira 70,000 a wata).

Ministan ya ce an samar da wannan alawus ne domin ƙarfafa bincike, tsara takardu da inganta gudanarwa, ta yadda manyan malamai za su fi mayar da hankali kan koyarwa, renon matasa da kirkire-kirkire.

Ya kuma tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatin Shugaba Tinubu za ta aiwatar da yarjejeniyar yadda ya kamata a karkashin shirin Renewed Hope Agenda, tare da ci gaba da tattaunawa da gyare-gyare a fannin ilimi.

Masu ruwa da tsaki na ganin yarjejeniyar za ta kawo sabon zamani na kwanciyar hankali da inganci a jami’o’in Najeriya, tare da dawo da daidaito a jadawalin karatu da kuma sabunta fata ga dalibai da iyaye.

Ministan ya yabawa tawagogin tattaunawar bangarorin biyu, karkashin jagorancin Alhaji Yayale Ahmed daga bangaren Gwamnatin Tarayya da Farfesa Pius Piwuna daga ASUU, tare da tsohon shugabancin ASUU na Farfesa Emmanuel Osodeke, bisa rawar da suka taka wajen samar da wannan nasara.

A karshe, Alausa ya ce tarihi ba zai tuna wannan rana a matsayin ranar kaddamar da yarjejeniya kawai ba, illa ranar da Najeriya ta zabi tattaunawa, gaskiya da jajircewar shugabanci a matsayin hanyar warware matsalolin da suka dade suna addabar kasa.

Da yarjejeniyar ta kammala, al’ummar Najeriya na fatan cewa zamanin rufe jami’o’i na dogon lokaci zai zama tarihi, yayin da ake sa ran samun kwanciyar hankali, ƙwarewa da gogayya da jami’o’in duniya a fannin ilimi.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
Next Post: Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci

Karin Labarai Masu Alaka

An Murkushe Wani Yunkurin Juyin Mulki A Jamhuriyar Benin Afrika
‘Yan Kungiyar Boko Haram Sun Yi Awon Gaba Da Mata 13 A Borno Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Guinea Bissau Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Kasar Benin Ta Nemi ‘Yan Kasa Su Kwantar Da Hankali Afrika
Kotun Tarayya Ta Yankewa Nnamdi Kanu Daurin Rai-da-Rai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Kashe Mutum 2 Da Suka Ba ‘Yan-Matan (GGCSS Maga) Kariya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • An Yi Fashin Kaguwa Da Dodon-Kodi Na Miliyoyin Dalar Amurka Amurka
  • An Kai Hari Kan Masu Hakar Ma’adanai A Kasar Mali Tsaro
  • Majalisar Dattawa Ta Wanke Janar Christopher Musa A Matsayin Minista Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Kai Shugaban Kasar Venezuela Kotu Amurka
  • Jirgin Sojojin Ruwa Yayi Gobara A Cross River Najeriya
  • Anfara Samun Sakamakon Wucin Gadi a Kasar Guinea Conakry Labarai
  • Kyaftin Na Super Eagles Ya Yi Ritaya. Wasanni
  • Dusar Kankara Ta Hana Jirage Tashi A Birnin Paris Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.