Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
Published: January 14, 2026 at 8:05 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayyar Najeriya da ASUU sun kulla yarjejeniya ta farko a tarihi domin kawo karshen yawan yajin aiki a jami’o’in Najeriya

A wani muhimmin mataki da ake ganin zai sauya fasalin ilimin jami’a a Najeriya, Gwamnatin Tarayya da Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Ƙasa (ASUU) sun kulla wata babbar yarjejeniya da nufin inganta jin daɗin malamai, tabbatar da zaman lafiyar aiki da kuma kawo ƙarshen yawan yajin aikin da ya shafe shekaru yana durƙusar da jami’o’in ƙasar.

An bayyana yarjejeniyar ta shekarar 2025 tsakanin Gwamnatin Tarayya da ASUU a ranar Laraba a Abuja, inda Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa, ya bayyana ta a matsayin wani sabon shafi a tarihin ilimin gaba da sakandare a Najeriya.

A cewarsa, yarjejeniyar ba rubutun takarda bane kawai, illa alamar dawo da amana, girmamawa da kwarin gwiwa ga tsarin jami’o’in ƙasar bayan shekaru na rashin tabbas da yajin aiki.

Ministan ya yabawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa daukar mataki na musamman wajen fuskantar matsalar da ta dade tana addabar jami’o’i, tana lalata jadawalin karatu tare da rusa makomar dalibai miliyoyi.

“Wannan ne karon farko da Shugaban Ƙasa mai ci ya tsaya tsayin daka wajen fuskantar wannan ƙalubale kai tsaye, ya ba matsalar kulawar shugabancin da ta dace,” in ji Alausa, yana mai cewa gwamnatin ta zaɓi tattaunawa maimakon rikici, gyara maimakon jinkiri, da warware matsala maimakon surutu.

Daya daga cikin manyan abubuwan da yarjejeniyar ta ƙunsa shi ne ƙarin albashin malaman jami’a da kashi 40 cikin 100, wanda Hukumar Albashi, Kuɗaɗen Shiga da Albashi ta Ƙasa (NSIWC) ta amince da shi Sabon tsarin albashin zai fara aiki daga ranar 1 ga Janairu, 2026.

A karkashin sabon tsarin, albashin malaman zai haɗa da CONUASS da kuma ingantaccen alawus na kayan aikin koyarwa da bincike (CATA). An ƙarfafa CATA domin tallafa wa wallafa mujallu, halartar taruka, amfani da intanet, rajistar ƙungiyoyin ƙwararru da rubuce-rubucen littattafai, domin ƙara gogayya da rage guduwar ƙwararru zuwa ƙasashen waje.

Haka kuma, yarjejeniyar ta sake tsara alawus-alawus guda tara na Earned Academic Allowances, inda aka fayyace su sarai tare da danganta su kai tsaye da ayyukan da ake yi kamar kula da daliban digirin digirgir, aikin asibiti, jarrabawa da shugabancin harkokin ilimi.

A wani sabon salo da ba a taba gani ba a tsarin jami’o’in Najeriya, Gwamnatin Tarayya ta amince da wani alawus na musamman ga manyan malaman jami’a, wato Farfesoshi da Masu Karatu (Readers).

A karkashin wannan tsari, Farfesoshi za su rika karɓar naira miliyan 1.74 a shekara (naira 140,000 a wata), yayin da Readers za su karɓi naira 840,000 a shekara (naira 70,000 a wata).

Ministan ya ce an samar da wannan alawus ne domin ƙarfafa bincike, tsara takardu da inganta gudanarwa, ta yadda manyan malamai za su fi mayar da hankali kan koyarwa, renon matasa da kirkire-kirkire.

Ya kuma tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatin Shugaba Tinubu za ta aiwatar da yarjejeniyar yadda ya kamata a karkashin shirin Renewed Hope Agenda, tare da ci gaba da tattaunawa da gyare-gyare a fannin ilimi.

Masu ruwa da tsaki na ganin yarjejeniyar za ta kawo sabon zamani na kwanciyar hankali da inganci a jami’o’in Najeriya, tare da dawo da daidaito a jadawalin karatu da kuma sabunta fata ga dalibai da iyaye.

Ministan ya yabawa tawagogin tattaunawar bangarorin biyu, karkashin jagorancin Alhaji Yayale Ahmed daga bangaren Gwamnatin Tarayya da Farfesa Pius Piwuna daga ASUU, tare da tsohon shugabancin ASUU na Farfesa Emmanuel Osodeke, bisa rawar da suka taka wajen samar da wannan nasara.

A karshe, Alausa ya ce tarihi ba zai tuna wannan rana a matsayin ranar kaddamar da yarjejeniya kawai ba, illa ranar da Najeriya ta zabi tattaunawa, gaskiya da jajircewar shugabanci a matsayin hanyar warware matsalolin da suka dade suna addabar kasa.

Da yarjejeniyar ta kammala, al’ummar Najeriya na fatan cewa zamanin rufe jami’o’i na dogon lokaci zai zama tarihi, yayin da ake sa ran samun kwanciyar hankali, ƙwarewa da gogayya da jami’o’in duniya a fannin ilimi.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
Next Post: Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci

Karin Labarai Masu Alaka

Jami’an Tsaro Sun Dakile Safarar Makamai Daga Jos Zuwa Jihar Neja Afrika
An Gabatar Da Sabbin Kudurorin Kare Muhalli Da Gandun Daji A Gombe Afrika
Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
Yau Shekaru 60 Da Kisan Gilla Ga Sir. Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
NANPAN Ta Wayar Da Al’umma Kan Amfanin Shayar Da Jarirai Nono Kaɗai Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jami’an Tsaro Na Amfani Da Damar Su Wajen Cin Zarafin Jama’a Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Matar El-Rufai Ta Roƙi Tinubu Ya Tabbatar An Yi Wa Mijinta Adalci Afrika
  • Galatasaray Ta Yi Watsi Da Tayin €150m Daga Al-Hilal Kan Victor Osimhen Wasanni
  • Shugaba Putin Ya Bukaci Kawo Karshen Yaki Da Iran Afrika
  • Netanyahu: Zamu Kashe Dala Billiyan $110 Cikin Shekaru Hudu Don Kera Makamai Sauran Duniya
  • Birtaniya Zata Hana Jiragen Ruwan Rasha Wucewa Afrika
  • Kungiyar Enyimba: Bamu Da Niyyar Rage Albashin ‘Yan-Wasa Wasanni
  • FIFA, Ta Raba Jaddawalin Rukuni Na Gasar Kofin Duniya 2026. Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.