Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Wasu Zakaru Da Suka Samu Karramawar Hukumar CAF Ta Afrika
Published: November 20, 2025 at 2:29 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

A Laraban nan 19 ga watan Nuwambar 2025, ne hukumar ƙwallon ƙafa ta Afirka, wato Confederation of African Football (Caf) ta bayar da kyautar gwarzon ɗan ƙwallon kafa na nahiyar afirka ta shekarar 2025, inda Achraf Hakimi, dan wasan kasar Morocco ya lashe kyautar.

Bikin da ya gudana a jami’ar Mohammed VI Polytechnic University (UM6P) da ke Rabat, babban birnin Morocco. Ana bayar da wannan kyautar ne duk shekara ga daidaikun ‘yanwasa da sukayi kwazo, da kuma tawagogi domin jinjina musu kan bajintar da suka nuna a shekarar a fadin nahiyar Afirka.

Ana zaben gwarzon dan kwallo daga bangaren maza da mata, da masu horarwa, da kungiyoyi, dama sashin matasa. Ga jerin sunayen wadanda suka lashe kyautar CAF bana 2025:

Gwarzon dan wasan Afirka bangaren maza, Achraf Hakimi dan kasar Morocco mai buga wa ƙungiyar kwallon kafa ta Paris St Germain,

Muhammed Sala daga kasar Masar mai buga wa ƙungiyar kwallon kafa ta Liverpool, shine ya zamo na biyu, Victor Osimhen dan kasar Najeriya mai taka leda a ƙungiyar Galatasaray shine a mataki na uku.

Caf ta zabe Achraf Hakimi ne bisa taimakawa da yayi wa kungiyar sa ta PSG ta lashe kofin Champions League da babbar gasar Ligue 1 da Coupe de France har ma da Uefa Super Cup duk a cikin wannan shekarar.

Dan wasan ya kafa tarihi inda ya zamo dan wasa na farko a kasar Morocco tun bayan shekaru 27 da Mustapha Hadji ya lashe a 1998, haka kuma ya kasan ce mai tsaron baya na farko bayan shekaru 52 da ya lashe Kyautar, bayan Bwanga Tshimen dan wasan Kasar Zaire, da ya lashe a 1973.

A bangaren mata ma ‘yar wasan Afirka ta shekara: Ghizlane Chebbak daga kasar Morocco kuma ita ce mai tsaron raga ba kulub din Al-Hilal, ta Saudiya.

Ga wasu jerin sunayen wadanda suka samu Kyautar.

‘Yar wasan tsakiya ta shekara: Fiston Mayele

Mafi kyawon mai tsaron raga: Yassine Bounou

Mafi kyawon mai tsaron raga ta mace: Chiamaka Nndozie

Mafi kyawon matashin ɗan wasa: Othmane Maamma

Mafi kyawon matashiyar ‘yar wasa mata: Doha El Madani

Kocin Shekara: Bubista

Ƙungiyar shekara: Morocco U-20

Ƙungiyar shekara ta mata: Najeriya

Ƙungiyar shekara: Pyramids FC.

Mafi kyawon alkalin wasa na maza na CAF: Omar Artan

Mafi kyawon alkalin wasa ta mata a CAF: Shamirah Nabadda

Sai kuma Kyautar CAF hukumar ta karrama shugabannin kasashe uku saboda gudummawar da suka bayar ga ci gaban ƙwallon ƙafa a Afirka. Shugaban Kenya William Ruto, shugaban Tanzania Samia Suluhu Hassan.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/11/RAHOTON-WASANNI-SAFE-20-11-2025.mp3
Wasanni

Post navigation

Previous Post: Shirin Dare 2030 UTC Yau Laraba 11.19.2025
Next Post: Trump Da Bin Salman Da Wasu Kasashe Za Su Sa Hannu A Rikicin Sudan

Karin Labarai Masu Alaka

Umar Ya Lashe Kyautar Gwarzon ‘Dan-Wasa Na 2025 Wasanni
Real Madrid: Ta Kori Xabi Alonso Bayan Rashin Nasara A Wasan Kofin Sfaniya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
CAF Ta Fara Binciken Rikicin Bayan Wasa Tsakanin Algeria Da Najeriya Wasanni
Salmanu: Ci Gaban Wikki Tourist FC Shine A Gaba Na Wasanni
Kocin Zambia Na Mata Ba Lafiya Labarai
Motsepe, Daga 2028 AFCON Zata Sauya Daga Shekaru Biyu Zuwa Hudu Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ko Meye Gaskiyar Rade-Radin Zanga-Zanga A Jos Dake Jihar Filato Labarai
  • Darajar Kudin Afirka Ta Kudu Ya Tashi Afrika
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Juma’a 11.21.2025 Rediyo
  • Mala Buni: Zai Jagoranci Kwamitin Sassanci Na Jam’iyar APC Labarai
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Alhamis 11.20.2025 Rediyo
  • Anyi Jefe-Jefe Yayin Rangadin Messi, A Indiya Wasanni
  • Wani Dan Bindiga Ya Harbi Dakarun Tsaron Cikin Gida Su Biyu A Washington DC Labarai
  • Farashin Danyen Mai Ya Farfado Fiye Da Kashi Daya Sauran Duniya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.