Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

An Kubutar Da ‘Yan Matan Sakandire Su 24 Na Jihar Kebbi
Published: November 25, 2025 at 8:00 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Shugaban Najeriya ya bada sanarwar cewa an kwato dukkan ‘yan mata 24 da aka sace daga wata makarantar sakandaren mata ta gwamnati dake Jihar Kebbi a Arewa maso yammacin kasar.

An sace wadannan dalibai mata ne a ran 17 ga watan Nuwamba, inda a lokacin ‘yan sanda suka ce su 25 aka sace.

Wata sanarwar da aka bayar yau Talata ta ambaci shugaba Bola Ahmed Tinubu yana fadin cewa an kwato dukkan dalibai 24 da aka sace. Ba a yi karin haske kan yadda aka kwato su ba.

Shugaba Tinubu yace yayi farin cikin cewa an samo wadannan ‘yan mata 24, yana mai cewa tilas ne a yanzu a dauki matakan tabbatar da cewa irin wannan abu bai sake faruwa ba a wuraren da suke fuskantar matsalolin tsaro ba.

Wannan hari na Kebbi na daga cikin hare-haren sace mutane masu yawa da aka yi cikin ‘yan kwanakin nan a Najeriya.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Jagorancin Wikki Tourist FC Na Samun Yabo
Next Post: Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Kasashen Duniya Sunyi Tir Da Hambarar Da Gwamnatin Venezuela Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kasar Uganda Ta Tsare ‘Yan Jam’iyyun Adawa Dubu Biyu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Nnamdi Kanu Zai Daukaka Kara Har Zuwa Kotun Koli Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Aliko Dangote: Faruk Ahmed Ya Ci Amanar ‘Yan Najeriya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sojin Ukraine Sun Janye Daga Gabashin Kasar Amurka
  • Eberechi Eze Ba Zai Buga Wasannin Da Ingila Za Tayiba Arteta Wasanni
  • Isra’ila Ta Cire Sunayen Wasu Mutane Biyu Cikin Wadanda Take Fako Afrika
  • Shugaba Tinubu Yakarawa Mambobin ASUU Kashi 40 Na Albashi Najeriya
  • Majalisar Dokokin Kamaru Ta Amince Da Wasu Sauye Sauye Afrika
  • Kotun Amurka Tana Tuhumar Wani Dan Jarida Amurka
  • Iran Tana Duba Yiwuwar Cimma Yarjejeniya Da Amurka Afrika
  • Kamfanonin Jiragen Sama Suna Fama Da Karin Farashin Mai Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.