Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno
Published: December 18, 2025 at 9:00 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Mayakan Boko Haram sun sace sabon mataimakin shugaban karamar hukuma da kansiloli a jihar Borno dake arewacin Najeriya

Wasu da ake zargin mambobin kungiyar Boko Haram ne sun sace sabon Mataimakin Shugaban Karamar Hukumar Biu da wasu kansiloli biyu, a kan hanyar Kamuya Buni Yadi, a Jihar Borno.

Majiyoyi da ke kusa da iyalansu sun bayyana sunan Mataimakin Shugaban a matsayin Alhaji Saidu. Kansilolin biyu masu wakiltar mazabun Zarawuyaku da Miringa.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa an zaɓi wadanda aka sace ne kwanaki biyar da suka gabata, a zaben kananan hukumomi da aka gudanar ranar Asabar da ta wuce.

Daya daga cikin majiyoyin ya bayyana cewa lamarin ya faru ne da yammacin ranar Laraba, kuma ya shafi wasu matafiya da ke cikin wata motar Hizbah Hummer.

“Gaskiya ne, Alhaji Saidu da kansilolin biyu an sace su ne da hannun wadanda ake zargin ‘yan Boko Haram/ISWAP ne, a tsakanin kauyen Kamuya da hanyar Buni Yadi.

“An sace su tare da wasu fasinjoji da ba a tantance su ba, wadanda ke tafiya cikin wata motar Hizbah daga garin Potiskum na Jihar Yobe zuwa Biu.

“Daya daga cikin kansilolin da aka sace shi ne tsohon Mataimakin Shugaban Karamar Hukumar Biu na nan kusa kuma muna rokon gwamnati da hukumomin tsaro su kara kaimi wajen ceto su da sauran wadanda aka kama” in ji shi.

Kokarin jin ta bakin kakakin rundunar ‘yan sanda ta Jihar Borno, ASP Nahum Kenneth Daso, bai yi nasara ba, domin ba a samu damar tuntubarsa ta waya ba, haka kuma bai amsa sakonnin da aka aike masa ba.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: A Kowacce Rana Kasar China Tana Sayan Danyen Mai Ganga Dubu 600 Daga Kasar Venezuela
Next Post: Gwamnatin Najeriya Ta Dauki Matakai Don Farfaɗo Da Maɗaba’ar Gwamnati

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Ta’adda Sun Tarwatsa Wani Kauye A Jihar Sakkwato Tsaro
Masar Ta Jibge Jiragen Yaki Marasa Matuka Afrika
Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Gombe Ya Ziyarci Pindiga Labarai
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Kauyuka Dake Yammacin A Najeriya Najeriya
Sojin Israela Sunkai Hari Kan Falatsinawa Tsaro
Nuhu Ribadu Ya Mika Yara 130 Da Aka Kubutar Ga Gwamna Bago Tsaro

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030
  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo
  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • Ana Jimamin Mutuwar Giwa Mai Shekaru Kusan 60 A Kasar Kenya Sauran Duniya
  • Sojin Najeriya Da ‘Yan Ta’adda Sunyi Taho Mugama Najeriya
  • Shugaba Tinubu ya mika sunayen Sabbin Shugabannin NMDPRA da NUPRC Bayan Murabus Din Farouk Ahmad Da Gbenga Komolafe Najeriya
  • Kasar Sham Ta Sallami Wasu Fararen Hula Labarai
  • Yau Litinin Za’a Mika Daliban Ga Iyayen Su Labarai
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Litinin 11.17.2025 Rediyo
  • Kasar Netherland Ta Mayarwa Masar Mutum Mutumin Tarihi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.