Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno
Published: December 18, 2025 at 9:00 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Mayakan Boko Haram sun sace sabon mataimakin shugaban karamar hukuma da kansiloli a jihar Borno dake arewacin Najeriya

Wasu da ake zargin mambobin kungiyar Boko Haram ne sun sace sabon Mataimakin Shugaban Karamar Hukumar Biu da wasu kansiloli biyu, a kan hanyar Kamuya Buni Yadi, a Jihar Borno.

Majiyoyi da ke kusa da iyalansu sun bayyana sunan Mataimakin Shugaban a matsayin Alhaji Saidu. Kansilolin biyu masu wakiltar mazabun Zarawuyaku da Miringa.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa an zaɓi wadanda aka sace ne kwanaki biyar da suka gabata, a zaben kananan hukumomi da aka gudanar ranar Asabar da ta wuce.

Daya daga cikin majiyoyin ya bayyana cewa lamarin ya faru ne da yammacin ranar Laraba, kuma ya shafi wasu matafiya da ke cikin wata motar Hizbah Hummer.

“Gaskiya ne, Alhaji Saidu da kansilolin biyu an sace su ne da hannun wadanda ake zargin ‘yan Boko Haram/ISWAP ne, a tsakanin kauyen Kamuya da hanyar Buni Yadi.

“An sace su tare da wasu fasinjoji da ba a tantance su ba, wadanda ke tafiya cikin wata motar Hizbah daga garin Potiskum na Jihar Yobe zuwa Biu.

“Daya daga cikin kansilolin da aka sace shi ne tsohon Mataimakin Shugaban Karamar Hukumar Biu na nan kusa kuma muna rokon gwamnati da hukumomin tsaro su kara kaimi wajen ceto su da sauran wadanda aka kama” in ji shi.

Kokarin jin ta bakin kakakin rundunar ‘yan sanda ta Jihar Borno, ASP Nahum Kenneth Daso, bai yi nasara ba, domin ba a samu damar tuntubarsa ta waya ba, haka kuma bai amsa sakonnin da aka aike masa ba.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: A Kowacce Rana Kasar China Tana Sayan Danyen Mai Ganga Dubu 600 Daga Kasar Venezuela
Next Post: Gwamnatin Najeriya Ta Dauki Matakai Don Farfaɗo Da Maɗaba’ar Gwamnati

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Kebbi Ta Samu Tankokin Yaki Tsaro
CAN: Da Alamu Daliban St. Mery Na Cikin Koshin Lafiya Najeriya
Kasashen Cambvodia Da Thailand Sun Kulla Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Tsaro
Gwamnatin Tarayya Ta Samu Nasarar Ceto Wasu Daliban St. Mary’s Tsaro
Tinubu: Zamu Kara Kyautata Samar Da Kayan Aiki Ga Jami’an Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Damke Wani Likita Da Ke Taimakawa ‘Yan-Ta’adda Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Fintiri: Zamu Maida Jihar Adamawa Sabuwar Duniya
  • Gwamnatin Najeriya Ta Dauki Matakai Don Farfaɗo Da Maɗaba’ar Gwamnati
  • Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno
  • A Kowacce Rana Kasar China Tana Sayan Danyen Mai Ganga Dubu 600 Daga Kasar Venezuela
  • Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Jam’iyyar PDP Na Kara Tsunduma Cikin Mawuyacin Hali Shirye-Shirye
  • Kocin Zambia Na Mata Ba Lafiya Labarai
  • Sanyin Hunturu Yayi Ajalin ‘Yan Cirani A Morocco Afrika
  • EFCC Ta Tsare Tsohon Minista Abubakar Malami Tsaro
  • Kasar Amurka Takara Saka Takunkumi Akan Kasar Venezuela Amurka
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Alhamis 11.20.2025 Rediyo
  • ‘Yan Wasan Kwallon Kafar Najeriya A Shirye Suke Wasanni
  • Nnamdi Kanu Ya Nemi A Mayar Da Shi Abuja Daga Gidan Yarin Sokoto Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.