Jami’an tsaro a jihar Borno a Najeriya sun kama wasu mutane 5 da ake zargi da harba bindiga, da harsashin ta ya samu wata yarinya me shekaru 14, yayi sanadiyar rayuwar ta, a lokacin taron wani biki.
Rahotanni sun bayyana cewa ‘yan bijilante ne ake zargin sun harba bindigar da ya samu yarinya a gidan mahaifan ta dake harabar asibitin koyarwa na Maiduguri.
Jami’in labarai na rundunar sojojin Operation Hadin kai Lt. Col. Sani Uba yace dakarun su ne, tare da ‘yan kato da gora suka kama mutane 5 din da ake zargi.


