Pakistan da Afghanistan sun fada ranar Litinin cewa, dakarun su sun auna sansanonin juna daga tsallaken iyakokinsu, yayinda fada tsakanin kasashen biyu ya shiga kwana na biyar, wadda yake nuna rashin zaman lafiya a yankin da tuni yake fama da rikici sakamakon harin da Amurka da Isra’ila suka kai kan Iran, ita kuma Farisa ta maida martani.
Sai dai fadan bai zafafa ainun kamar a kwanakin farko ba, duk da haka babu alamun cewa kasashen biyu kawaye a baya, wadanda suke gaba da juna suna da wani shiri na janyewa da nufin neman sulhu ba.
Yakin ya samo asali ne lokacin da shugabannin Taliban a Afghanistan suka kaddamar da abunda suka kira ramuwar gayya kan wasu muradun Pakistan, saboda hari da Pakistan ta kai kan mayakan sakai a Afghanistan Mutane da yawa suka halaka a duka sassan biyu.


