Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Wata Mace Ta Mutu A Hannun ‘Yan-Fashin Daji, Wata Ta Haihu
Published: December 19, 2025 at 11:21 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Rahotanni daga Jihar Nejan Najeriya na nuna cewa wata mace daga cikin mutane 17 da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su ta tutu a hannun ‘yanfashin dajin.

Tun a ranar 1/8/2025 ‘yanbindigar suka kutsa garin Ibeto a karamar Hukumar Magama suka kwashe mutane goma sha bakwai 14 daga cikin su matane sai kuma maza uku.

Masu garkuwar bukaci kudin fansa na naira milyan 150 kafin su sako wadan nan mutane, kuma har ya zuwa wannan lokaci mutanen garin na Ibeto basu hada wadannan kudaden ba.

Muhammad Kabir mazaunin garin na Ibeto yace tabbas sun samu labarin mutuwar daya daga cikin matan, sannan kuma wata matar guda da aka wuce da ita da ciki ta haihu a ranar Laraban nan da ta gabata.

Har yau dai babu wani bayani mai karfi daga bangaren gwamnatin Jihar Nejan akan kokarin karbo wadannan mutane na garin Ibeto,

Sai dai Shugaban karamar Hukumar ta Magama Dr. Muhmud Muhammad yace matsalar tana damunsu kuma cikin ikon Allah zasu samu mafita.

Kwamishinan Ma’aikatar kula da manyan Makarantun Jihar Nejan Farfesa Yakubu Auna, yace amatsayin su na masu ruwa da tsaki a yankin suna kokarin ganin an samu nasarar karbo wadannan mutane.

Mutuwar wannan baiwa Allah ta Ibeto a hannun ‘yanbindigar dai yana wuwa ne a dai dai lokacin da Kwamishina a hukumar Zabe ta jihar Neja Barista Ahmed Muhammad Borgu da Kuma tsohon shugaban Hukumar bada Ilimi bai daya ta jihar Nejan Hon. Alhasan Bawa Niworu suka share kimanin watanni uku a hannun ‘yanfashin da a yanzu haka bayanai ke nuna masu garkuwar sun bukaci milyan 300 kafin su sako su.

A yanzu dai hukumomin Jihar Nejan sun maida hankali wajan kokarin kubutar da sauran yara kimanin 200 da akayi garkuwa dasu a makarantar St Mary mallakar Cocin Katolica dake garin Papiri duk a Jihar Nejan.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/12/WATA-MATA-TA-MUTU-A-HANNUN-YANBINDIGA.mp3
Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Shugaba Tinubu Ya Gargadi Gwamnoni Game Da Rike Kudaden Kananan Hukumomi Tare Kuma Da Bada Tabbacin Kafa ‘Yan Sandan Jihohi
Next Post: Rahoton MDD Yace An Kashe Fiye Da Farar 1000 A Sudan

Karin Labarai Masu Alaka

Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Matatar Man Dangote Zata Wadatar Da Najeriya Da Makota Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Ya Zamo Khalifan Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Ribadu: Najeriya Ce Kasa Daya Tilo Da Ke Tabbatar Da Demokraɗiyya A Sahel Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kamfanin Hakar Ma’adanai Na Kasar Kanada Ya Cigaban Da Aikinsa
  • Za’a Koyawa Yara Tarihin Shugaba Donald Trump Saboda Rayuwarsa Akwai Darasi Wajen Jajircewa Da Kwazo
  • Rahoton MDD Yace An Kashe Fiye Da Farar 1000 A Sudan
  • Wata Mace Ta Mutu A Hannun ‘Yan-Fashin Daji, Wata Ta Haihu
  • Shugaba Tinubu Ya Gargadi Gwamnoni Game Da Rike Kudaden Kananan Hukumomi Tare Kuma Da Bada Tabbacin Kafa ‘Yan Sandan Jihohi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • AFCON 2025, Jerin Abubuwan Da Aka Haramta Wa Magoya Baya Wasanni
  • FIFA Na Shirin Fadada Babban Na’urar VAR A Gasar Cin Kofin Duniya 2026. Wasanni
  • Iran Ta Tasa Keyar Wani Jirgi Shake Da Mai Sauran Duniya
  • Tsohon Minista Ngige Ya Shiga Komar EFCC Najeriya
  • Akalla Mutane 8 Sun Mutu Biyo Bayan Bindiga Da Wata Tanka Tayi Afrika
  • Baba Buhari Yayi Zargin Ansaka Masa Na’urar Tsaro Labarai
  • Akwai Bukatar Bincikar Umurnin Da Sakataren Tsaro Pete Ya Bada Amurka
  • Najeriya: Ba Don Leken Asiri Muka Tura Jirgin Yakin Mu Ba Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.