Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Netanyahu: Zamu Kashe Dala Billiyan $110 Cikin Shekaru Hudu Don Kera Makamai
Published: December 25, 2025 at 7:12 AM | By: Bala Hassan | Updated: December 25, 2025

Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu a laraba yace kasar bani yahudun, zata kashe kudi dala bilyan 110 cikin shekaru hudu masu zuwa, wajen kafa sashen kera makamai maizaman kansa domin kasar ta rage dogaro kan wasu kasashe wajen samun makamai.

“Zamu ci gaba da neman wasu muhimman bukatu, a hanu daya kuma zamu samar da makamai da kan mu, inji PM Netanyahu a lokacinda yake magana a bikin kaddamar da shirin.

Bana cewa kasa zata iya biyawa kanta bukatunta kachokam ba, amma zamu yi bakin kokarin mu waje ganin haka. “in ji shi.

Burin mu shine gina sashen kera makamai na kasar Isara’ila domin mu rage dogaro kan kasashe ciki harda kawayen mu.

A gefe daya kuma, Isra’ila ta fada a Laraban nan cewa, zata dauki fansa bayan da ta zargi Hamas da keta yarjejeniyar tsagaita wuta, bayanda wani sojanta ya sami rauni sakamakon wata fashewa a Gaza, sai dai hamas ta musanta zargin, tana mai cewa, fashewar daga wani makami ne da aka bari a wurin tun lokacinda ake bata kashi.

PM Netinyahu ya ma baci lamarin ne da ya auku a Rafah, inda Isra’ilan take daukar matakan soji a yayinda yake magana a wani bikin yaye daliban makarantar horasda sojojin sama na kasar, ya kara da cewa Hamas ta fito fili ta nuna cewa ba zata kwance damara ba, kamar yadda yake kunshe cikin yarjejeniyar da aka kulla na tsagaita wuta  a cikin watan Oktoba.

A wani gefe kuma, yan share wuri zauna na Isra’ila a wani dan karamin wuri da ake kira Or Meir, sun bayyana a shafukan Telegram shirin su na ci gaba da korar Falasdinawa a yankin.

Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Zelensky Na Buƙatar Ganawa Da Trump Domin Cimma Matsaya Kan Batutuwa Masu Sarƙaƙiya
Next Post: Amurka Ta Sanya Hanu Kan Yarjejeniyar Kiwon Lafiya Da Ƙasashen Madagascar, Saliyo, Botswana, Ethiopia

Karin Labarai Masu Alaka

Hamas Ta Mika Ma Isra’ila Gawar Daya Daga Cikin Mutane Biyu Sauran Duniya
Asusun IMF Zai Bawa Kasar Misra Lamunin Sama Da Dala Biliyan 2 Sauran Duniya
Somaliya: Ba Za Mu Dauki Wulakancin Donald Trump Ba! Sauran Duniya
Ukraine Ta Mika Wa Amurka Daftarin Yarjejeniya Da Rasha Sauran Duniya
Ukraine Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Tsarin Cimma Yarjejeniya Sauran Duniya
Rasha: Zamu Ba Gwamnatin Venezuel Gudunmawa Sauran Duniya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Majalisar Tarayya Ta Amince Da Mutane Uku A Matsayin Jakadun Kasashen Waje Labarai
  • Ana Jimamin Mutuwar Giwa Mai Shekaru Kusan 60 A Kasar Kenya Sauran Duniya
  • Tsananta Hukunci Ga Masu Fyade Kan Takaita Cin Zarafin Yara Labarai
  • A Hudubar Kirsimeti Paparoma Leo Ya Jajantawa Al’ummar Falatsinu A Yankin Zirin Gaza Amurka
  • Sakataren Gwamnatin Amurka Ya Bayyana Bawa Kungiyoyin Agaji Damar Kai Taimako Sudan Amurka
  • An Bude Gasar Kwallon Kafa Ta Mata A Najeriya NWFL 2025 Wasanni
  • Gwamnatin Gombe Ta Dauki Sabbin Matakan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sabon Magajin Garin New York Zai Soke Wasu Dokoki Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.