Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

An Kai Hari Kan Masu Hakar Ma’adanai A Kasar Mali
Published: January 5, 2026 at 8:21 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wasu da ake zargin ‘yan ta’adda ne sun kai farmaki wajen hakar ma’adanin gwal na Morila a kasar Mali karshen makon da ya wuce, inda suka kona kayayyakin aikin, kuma suka yi garkuwa da ma’aikatan gurin guda bakwai, kamar yadda wani jami’i a ma’aikatar ma’adanai ta kasar ya shaidawa kamfanin dillacin labarai na Reuters ranar Litinin.

Wannan harin yana nuni da kara tabarbarewar tsaro a Mali, wadda ita ce kasa ta uku da ta fi samar da gwal a Afirka, da ke yaki da ‘yan ta’adda da ke da alaka da kungiyar Al-Qaida, wadanda kan kai farmaki ga kadarori na tattalin arzikin kasa, da kayan zuba jari a kasashen waje.

Mutane dauke da makamai, sun kai farmaki inda aka hakar ma’adanin, wanda wani kamfanin kasar Amurka, Flagship Gold ya rattaba hannu kan yarjejeniyar kasuwanci a shekarar da ta gabata, a cewar wani me magana da yawun ma’aikatar hakar ma’adanai ta kasar Mali.

Wani da ke da masaniya a kan abun ya kara da cewa, sun kokkona kayayyakin aiki, sannan suka yi garkuwa da ma’aikata bakwai, amma duk sun sako su washegari da yamma.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: An Hana Yada Rahotannin Siyasa A Kasar Uganda
Next Post: An Kai Shugaban Kasar Venezuela Kotu

Karin Labarai Masu Alaka

Isra’ila Ta Kashe Babban Jami’in Tsaron Iran Ali Larjani Afrika
Jami’in Diflomasiyyar Da Ake Zargi Da Kisan Prime minister Ya Daukaka Kara Afrika
Tashoshin Mai Basa Iya Loda Mai A Rasha Labarai
An Kaiwa Sojojin Ghana Hari A Lebanon Afrika
Gwamnatin Tarayya Ta Samu Nasarar Ceto Wasu Daliban St. Mary’s Tsaro
Shugaba Trump Ya Bukaci Kasar Iran Ta Mika Wuya Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnonin Arewa Maso Yammacin Najeriya Sun Halarci Taron Inganta Makashi A Birnin Landan Afrika
  • Farashin Man Fetur Yakara Tashi Labarai
  • Hukumar Hisbah Ta Kona Barasar Dubban Nairori A Katsina Labarai
  • Ganduje Ya Nisanta Kansa Da Batan Dadiyata Labarai
  • Mizanin Tattalin Arzikin Najeriya Na 2024 Ya Karu Da Kashi 3.84% Labarai
  • Shugaban Mulkin Soja A Mali Ya Kirkiro Mukami Kamar Minista Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Zata Fara Gwajin Shan Kwaya Kafun Daukar Aiki Kiwon Lafiya
  • Gwamnatin Kano Ta Rufe Gidajen Bukukuwa Da Shakatawa Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.