Sojojin kasar Congo da wasu dakarun ‘yan tawaye masu marawa gwamnati baya sun kara shigowa yankin gabashin garin Uvira, a cewar mazauna garin ranar Litinin, wata daya kacal bayan da ‘yan tawayen M23, da Rwanda ke marawa baya suka mamaye garin, abin da ya wargaza kokarin kawo zaman lafiya da shugaban Amurka Donald Trump ke neman sasantawa.
Dakarun M23 sun shiga Uvira, garin da ke kusa da iyakar kasar Congo da Burundi, wanda kuma yake sansani me muhimmanci ga sojojin Congo, ranar 10 ga watan Disamba, kwanaki bayan shugaban Congo Felix Tshisekedi da shugaban Rwanda Paul Kagame suka gana da shugaban Amurka Donalad Trump a Washington don kara jaddada kudurin yarjejeniyar wanzar da zaman lafiya a yankunan su.
A watan Disamba, bayan da sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Rubio ya ce abinda Rwanda ke aikatawa a gabashin Congo da ke da arzikin ma’adanai, ya sabawa yarjejeniyar zaman lafiya da aka kulla, dakarun na M23 suka dau alwashin janyewa daga Uvira don bawa tattaunawa kan zaman lafiya dama


