Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Amurka Ta Gabatarwa Sassan Dake Yakar Juna A Sudan da Shirin Tsagaita Wuta
Published: November 26, 2025 at 4:04 PM | By: Nafisa Ahmad

Wakilin Amurka, Massad Boulos, ya ce Amurka ta gabatarwa da sassan dake yakar juna a kasar Sudan wani shiri na kulla tsagaita wuta, amma kuma babu daya daga cikin bangarorin da ya bayyana amincewarsa da shirin ya zuwa yanzu.

Boulos yace duk da cewa babu wanda ya nuna rashin yarda da abubuwan dake kumshe a cikin shirin da Amurka ta gabatar, rundunar sojojin Sudan ta shimfida wasu ka’idojinta wadanda yace ba za a iya cimmawa ba.

Mai yakar rundunar sojoji a wannan fadan, Rundunar Dakarun wucin gadi ta RSF, ta ayyana tsagaita wuta na radin kanta jiya Litinin kamar yadda Amurka ta nema. Amma a yau Talatar nan, rundunar sojojin Sudan ta ce ta fatattaki wani harin da aka kai kan wani sansaninta dake Babanusa a Jihar Kordofan ta yamma, inda a nan yanzu bakin daga take a yakin na Sudan.

A makon da ya shige shugaba Donald Trump yace zai sa baki domin ganin an kawo karshen  wannan fadan daya barke a tsakanin rundunar soja da ta RSF a watan Afrilun 2023 a sanadin gwagwarmayar neman shugabanci tsakanin sassan biyu. Wannan rikici ya haddasa bala’in yunwa mai tsanani da kashe-kashen kabilanci da kuma raba miliyoyi da matsugunansu.

A halin da ake ciki, kungiyar agaji ta likitoci mai suna Medicine Sans Frontier, ko MSF a takaice, ta fada a yau Talata cewa ta janye ma’aikatanta daga wani asibitin dake Darfur, a bayan da aka harbe wani mai tura keken daukar marasa lafiya har lahira.

Kungiyar tayi kira ga dakarun rundunar RSF dake rike da wannan yanki da su tabbatar da tsaron lafiyar ma’aikatan asibitin dake yankin tsakiyar Darfur.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Ukraine Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Tsarin Cimma Yarjejeniya
Next Post: Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Guinea Bissau

Karin Labarai Masu Alaka

Hari Akan Wata Mashaya Ya Rutsa Da Mutane 9 A Afirka Ta Kudu Afrika
An Gudanar Da Zanga-Zanga A Guinea-Bissau Afrika
Jiragen Saman Yakin Najeriya Suka Gurgunta Yunkurin Juyin Mulki A Benin Afrika
Shugaban Ƙasar China Zai Karbi Bakwancin Shugaban Koriya Ta Kudu Afrika
Gwamnatin Jamhuriyar Nijar Na Kokarin Inganta Harkokin Noman Kasar Afrika
An Damke Matasa Masu Gurza Kudaden Ketare Na Jabu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jam’iyar APC A Najeriya Ta Kaddamar Da Bada Shaidar Zama Dan Jam’iyyar Ta Na’ura Mai Kwakwalwa
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Anfara Tantance Lafiyar Maniyyatan Jihar Gombe Kiwon Lafiya
  • An Shirya Taron Horas Da Matasa Gabanin Wasan Motsa Jiki 2025 Wasanni
  • Jiragen Saman Yakin Najeriya Suka Gurgunta Yunkurin Juyin Mulki A Benin Afrika
  • Hukumar ICPC Ta Gayyaci Dangote Labarai
  • Gwamna Kefas Na Jihar Taraba Ya Karbi Shaidar Jam’iyar APC Siyasa
  • Kotun Tarayya Ta Yankewa Nnamdi Kanu Daurin Rai-da-Rai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Wani Jirgi Yayi Saukar Angulu Ba Shiri Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.