Matatar mai ta Dangote a Najeriya, wadda ita ce mafi girma a nahiyar Afirka, ta kara adadin mai dake zuwa kasashen Afirka da suke fama da matsalar shigowa da kayayyaki saboda yakin Iran, a cewar matatar Aliko Dangote a ranar Litinin.

Dangote yace matatar da take yin cikakken aikin tace mai na ganga 650,000 kowacce rana, ta taimaka wajen kawo sauki ga matsalar da aka shiga ciki a gida Nigeria da kuma fadin Afrika.
Yace matatar ta tura da tankokin mai 17 zuwa ga wasu kasashen Afirka, kuma shima takin zamanin da suke fitarwa ya karu, yayin da masu saye suke neman wuri daban dan samun shi.


