Jiya laraba wani alkali a kotun tarayya ya ja burki ma gwamnatin shugaba Donald Trump a wani yunkurin da take yi na kawo karshen kariya ga ‘yan kasar Ethiopia su fiye da dubu 5, kariyar da ta ba su iznin zama tare da yin aiki a nan Amurka.
Wannan hukunci da alkali Brian Murphy na kotun tarayya dake Boston ya yanke, shine kashi na baya bayan nan da Ma’aikatar tsaron cikin gida ta Amurka ta sha a kotu a yunkurin ta na kawo karshen Kariyar Wucin Gadi ga ‘yan gudun hijira daga kasashe 13, a wani bangaren ajandar Trump ta nuna kin jinin ‘yan gudun hijira.
Wannan kariya ta Wucin gadi, dokokin Amurka ne suka ba da ta ga duk wani dan gudun hijirar da aka fuskanci wani bala’i, ko yaki ko wani abu na tashin hankali a kasarsa ta asali. Kariyar tana ba wadanda suka same ta takardar izinin yin aiki tare da zama a Amurka ba tare da fuskantar kora ba.


