Majalisar Zartarwa a Tarayyar Najeriya (FEC) karkashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta amince da yin gyare-gyare ga tsarin yi wa kasa hidima (NYSC).
Ministan Matasa, Ayodele Olawande, ne ya bayyana hakan bayan taron majalisar da aka gudanar a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja a ranar Litinin.
Ya ce gyaran zai kunshi cikakken nazari da sake duba tsarin shirin na NYSC domin ya dace da bukatun zamani.
An kafa shirin NYSC a shekarar 1973 bayan yakin basasar Najeriya da nufin karfafa hadin kai da zumunci tsakanin matasa masu digiri daga sassa daban-daban na kasar.
Tsawon shekaru 53 da kafuwar shirin, NYSC ta taimaka wajen hada kan matasa da kuma inganta hadin kan kasa.
Sai dai ministan ya ce sauye-sauyen da suka faru a kasar cikin shekaru da dama sun sa ya zama dole a sake fasalin shirin, yana mai cewa bukatun Najeriya sun canza, kuma ana sa ran manufofin NYSC su ma su dace da sabon yanayin da ake ciki.


