Masana harkokin lafiya sun shawarci al’umma da su rika kula da lafiyar idanunsu tare da yin gwajin ido a kai a kai domin kaucewa kamuwa da cututtukan da kan haddasa makanta.
Sun bayyana cewa cututtukan ido ba wai kawai suna shafar lafiyar mutum ba ne, har ma suna jefa iyalai cikin matsin tattalin arziki, saboda mai fama da makanta kan rasa damar gudanar da wasu ayyukansa na yau da kullum tare da dogaro da ‘yan’uwa wajen kulawa da shi da kuma sayen magunguna.

Bayanai sun nuna cewa kimanin mutane miliyan 48 ne ke fama da nau’o’in cututtukan ido a duniya, yayin da masana ke hasashen adadin zai karu zuwa miliyan 61 nan da shekarar 2050 idan ba a dauki matakan kariya ba.
A wani yunkuri na inganta lafiyar ido, Kungiyar Christian Health Association of Nigeria (CHAN) ta shirya duba lafiyar idanun ‘yan jarida a Jihar Filato, domin tabbatar da cewa aikin da suke yi da na’urorin zamani bai jefa lafiyar idanunsu cikin hadari ba.
Daraktan kungiyar CHAN, Dakta Suleiman Mshelia, ya ce sakaci wajen kula da ido na daga cikin manyan abubuwan da ke haddasa matsalolin gani, musamman yayin da mutum ke kara shekaru.

Shi ma Farfesa Ezekiel Major Adeyi na Jami’ar Jos ya bayyana cewa ya shafe shekaru 30 yana fama da matsalar ido, amma saboda bin shawarwarin likitoci da kula da idanunsa, har yanzu yana iya karatu da rubutu duk da kusantar sa shekara 70 da haihuwa.
A nata bangaren, ‘yar jarida Hadiza Ahmad Hassan ta ce shirin ya kara mata ilimi kan yadda za ta kula da idanunta da kuma wayar da kan al’umma game da muhimmancin kula da lafiyar ido.
Masanan sun jaddada cewa yin gwajin ido a asibiti lokaci-lokaci na iya rage yawan masu makanta da kusan kashi uku cikin hudu, tare da yin kira ga gwamnati da ta hada kula da lafiyar ido cikin ayyukan kiwon lafiya domin saukaka wa al’umma samun wannan muhimmin ayyuka
Wakiliyar GTA Hausa Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton Daga Jos


