Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

CHAN Ta Duba Lafiyar Idanun ‘Yan Jarida A Filato
Published: July 19, 2026 at 5:07 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Masana harkokin lafiya sun shawarci al’umma da su rika kula da lafiyar idanunsu tare da yin gwajin ido a kai a kai domin kaucewa kamuwa da cututtukan da kan haddasa makanta.

Sun bayyana cewa cututtukan ido ba wai kawai suna shafar lafiyar mutum ba ne, har ma suna jefa iyalai cikin matsin tattalin arziki, saboda mai fama da makanta kan rasa damar gudanar da wasu ayyukansa na yau da kullum tare da dogaro da ‘yan’uwa wajen kulawa da shi da kuma sayen magunguna.

Bayanai sun nuna cewa kimanin mutane miliyan 48 ne ke fama da nau’o’in cututtukan ido a duniya, yayin da masana ke hasashen adadin zai karu zuwa miliyan 61 nan da shekarar 2050 idan ba a dauki matakan kariya ba.

A wani yunkuri na inganta lafiyar ido, Kungiyar Christian Health Association of Nigeria (CHAN) ta shirya duba lafiyar idanun ‘yan jarida a Jihar Filato, domin tabbatar da cewa aikin da suke yi da na’urorin zamani bai jefa lafiyar idanunsu cikin hadari ba.

Daraktan kungiyar CHAN, Dakta Suleiman Mshelia, ya ce sakaci wajen kula da ido na daga cikin manyan abubuwan da ke haddasa matsalolin gani, musamman yayin da mutum ke kara shekaru.

Shi ma Farfesa Ezekiel Major Adeyi na Jami’ar Jos ya bayyana cewa ya shafe shekaru 30 yana fama da matsalar ido, amma saboda bin shawarwarin likitoci da kula da idanunsa, har yanzu yana iya karatu da rubutu duk da kusantar sa shekara 70 da haihuwa.

A nata bangaren, ‘yar jarida Hadiza Ahmad Hassan ta ce shirin ya kara mata ilimi kan yadda za ta kula da idanunta da kuma wayar da kan al’umma game da muhimmancin kula da lafiyar ido.

Masanan sun jaddada cewa yin gwajin ido a asibiti lokaci-lokaci na iya rage yawan masu makanta da kusan kashi uku cikin hudu, tare da yin kira ga gwamnati da ta hada kula da lafiyar ido cikin ayyukan kiwon lafiya domin saukaka wa al’umma samun wannan muhimmin ayyuka

Wakiliyar GTA Hausa Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton Daga Jos

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/07/AUD-20260719-WA0026.mp3
Afrika, Kiwon Lafiya, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Tinubu Zai Gabatar Da Jawabi ga Shugabannin Duniya A Taron UNGA
Next Post: Shari’ar Ta’addanci: Manyan Jagororin Ansaru Biyu Sun Amsa Laifi A Abuja

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumar Zabe Ta Saukaka Gudanar Da Rijistar Katin Zabe A Najeriya Labarai
Dakarun Sakai A Kasar Sudan Sun Kashe Mutane 28 A Wani Farmaki Afrika
Wakilan Rasha Da Ukraine Sun Tattauna A Abu Dhabi Ranar Juma’a Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kasar Congo Ta Dau Alwashin Bin Tsari Wajen Rarraba Ma’adanai Afrika
Thailand Da Cambodia Sun Fara Tattauunawa Kan Batun Tsagaita Wuta Labarai
Sakataren Kungiyar NATO Yayi Magana Da Hukumomin Kasashe Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura Labarai
  • Ana Zargin Tsohon Shugaban Kasar Philippines Da Ta’addaci A Lokacin Mulkinsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Fadar Shugaban Ƙasan Najeriya Ta Musanta Wani Labarin ƙarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Ta Kai Wasan Kusa Da Na Karshe A Wasan Dambe Na Matasan Afirka Wasanni
  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027 Afrika
  • Kasar Faransa Zata Bunkasa Nukiliyarta Afrika
  • Farashin Mai Yana Cigaba Da Karuwa Afrika
  • Ministan Tsaron Najeriya Badaru Yayi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.