Shugaban Ƙasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu, ya amince da faɗaɗa tsarin Rundunar Sojin Ƙasa ta Najeriya daga rukuni takwas zuwa goma sha biyu, tare da ba da izinin ɗaukar sabbin sojoji dubu 28 domin ƙarfafa tsaron ƙasa da inganta ƙarfin rundunar wajen fuskantar ƙalubalen tsaro.
Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Yaɗa Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Alhamis.
Sanarwar ta ce matakin na daga cikin ƙudirin gwamnatin Shugaba Tinubu na sake fasalin Rundunar Sojin Ƙasa domin ƙara mata inganci wajen gudanar da ayyuka, inganta tsarin jagoranci da umarni, da kuma hanzarta mayar da martani ga barazanar tsaro a sassa daban-daban na ƙasar.
A cewar sanarwar, gwamnatin tarayya ta kuma amince da ɗaukar sabbin sojoji dubu 28, tare da ci gaba da samar da manyan kayan aikin soja na zamani, inganta walwalar jami’ai da sojoji, da kuma ƙarfafa shirye-shiryen zamanantar da rundunar.
Sabon tsarin zai sanya Rundunar Sojin Ƙasa ta kasance da rukuni goma sha biyu da za su kasance a muhimman yankuna na ƙasar. Hedikwatar Runduna ta 3 da ke Jos za ta ci gaba da kula da ayyukan soji a jihohin Filato, Bauchi da Gombe.
Haka kuma, za a kafa sabbin hedikwatocin rundunoni a Makurdi, Ilorin, Jalingo da Benin City.
Sanarwar ta bayyana cewa aiwatar da wannan sabon tsari za a yi shi kashi biyu. Kashi na farko, wanda ya haɗa da kafa Rundunoni na 5 da na 9 da na 10 tare da sake tsara wasu rundunonin da ake da su, ana sa ran kammala shi kafin ƙarshen watan Satumban 2026. Kashi na biyu kuma, wanda ya ƙunshi kafa Runduna ta 83 da ƙarin sake fasalin rundunar, ana sa ran kammala shi kafin ƙarshen watan Disamban shekarar 2026.
Har ila yau, Shugaba Tinubu ya yabawa Babban Hafsan Sojin Ƙasa, Laftanar Janar Waidi Ibrahim Shuaibu, da daukacin jami’ai da dakarun Rundunar Sojin Ƙasa bisa jajircewarsu da ƙwarewarsu wajen kare ikon Najeriya da kuma tabbatar da tsaron ƙasar.
Shugaban ya sake jaddada aniyar gwamnatinsa ta ci gaba da zuba jari a harkokin rundunonin tsaro, domin tabbatar da cewa suna da isassun kayan aiki, ƙwararrun ma’aikata da ƙarfin da zai ba su damar kare rayuka, dukiyoyi da martabar ƙasar.


