Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Akwai Bukatar Hukunci Mai Tsanani Ga Duk Wanda Yayi Fyade
Published: December 7, 2025 at 4:48 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Wassu ‘yan mata da aka ci zarafinsu ta hanyar yin musu fyade, sun karfafawa gwiwan sauran mata da dukkan wadanda ke fuskantar kuntatawa, su rika fitowa karara suna bayyana matsalarsu ga hukumomi da suak dace, don samun adalci.

A ci gaba da yakin neman kawar da duk wani nau’i na cin zarafi, musamman ma ga mata, a kwanaki goma sha shida da majalisar dinkin duniya ta kebe, kungiyar ‘yan jarida mata, reshen jahar Filato ta gabatar da wassu ‘yan mata biyu ga asibitin kwararru na jahar, don ci gaba da duba lafiyarsu.

Chidimma Augustine wacce aka yi wa fyade, ta kuma sami ciki, da yanzu haka ke wata biyar, tace wanda ya mata fyaden ya ki amincewa, balle ma ya dauki nauyin kaita awu, wanda ya cewarta yace yana bin mahaifinta bashin naira dubu biyar.

Ita ma Justina Dusu wanda tace saurayin ta ne ya mata ciki, bayan ta bayyana masa halin da take ciki, ya rufa tad a bugu da sara da adda har ya fasa mata kwayar ido.

Shugaban kungiyar ‘yan jarida mata, reshen jahar Filato, Madam Grace Akwe Gotip tace kungiyar na bukatar hadin kan al’umma wajen hana cin zarafin mata da taimaka wa wadanda suka fuskanci cin zarafi.

Shima shugaban wata kungiyar matasa dake yaki da cin zarafin al’umma, YIAHVA, Mr Pwakim Jacob Choji, yace tilas sai hukumomi sun aiwatar da dokoki masu tsauri, don kau da cin zarafin al’umma.

Dakta Sa’idu Barnabas, wanda ya karbi ‘yan matan a madadin shugaban asibitin, yace za su yi duk mai yiwuwa wajen tabbatar da ‘yan matan sun sami kulawa mai nagarta.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/12/CIN-ZARAFIN-MATA.mp3
Najeriya

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery
Next Post: Gwamnatin Bauchi: Ba Zamu Bude Makarantu Ba Sai 2026

Karin Labarai Masu Alaka

An Kashe Mutane 25 Yayin Kai Wasu Hare Hare Jihar Adamawa Labarai
Gwamnatin Sokoto Tabada Umarnin Biyan Albashin Watan Fabrairu Labarai
Kananan Hukumomi Na Kokarin Karbar Kudadensu Daga Jihohi Najeriya
Tinubu Ya Rantsar Da Shugabar Hukumar FCC Najeriya
Ma’aikatan Tattara Kudin Haraji Sunyi Rikici Da Masu Babura A Bauchi Najeriya
Gwamna Ododo Ya Gargadi Sarakunan Gargajiya Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ronaldo Da Messi Ka Iya Hadu A Gasar Cin Kofin Duniya: Ta Ya Ya ? Wasanni
  • Dan Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya Atiku Abubakar Ya Shiga Jam’iyyar APC Siyasa
  • Abun Da Kuke Buƙatar Sani Game Da Gasar Cin Kofin Ƙasashen Afirka 2025 Wasanni
  • Kasar Ghana Ta Umarci ‘Yan Kasar Su Daina Zuba Jari A Kasashen Waje Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Na Shirin Yin Zamiya Don Biyan Bashi Labarai
  • Wasu Mutane 15 Sun Rasa Rayukan Su A Gabashin Kwango Afrika
  • Hawan Nasarawa A Jihar Kano Afrika
  • China Ta Yi Kira Da Kasashen Gabas Ta Tsakiya Su Hada Kai Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.