Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Tayi Barazanar Rage Tallafinta Wa Sudan Ta Kudu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai

Ana Gudanar Da Zanga-Zangar Adawa Da Gwamnati A Kasar Tunisiya
Published: December 14, 2025 at 6:04 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

‘Yan raji da jigogin hamayya na kasar Tunisiya sun fantsama kan titunan kasar ranar asabar suna zanga-zangar hadin guiwa da ba a saba ganin irinta ba, ta adawa da shugaba Kais Saied, suna bukatar da a kawo karshen mulkin mutum guda da maido da dimokuradiyya a kasar.

Zanga-zangar dai ta biyo bayan wadda aka shafe makonni uku ana yi, kuma ta nuna airin karin hadin kan da ake samu a tsakanin kungiyoyin hamayya da na al’umma wajen adawa da matakan da ba a taba gani ba a kasar na murkushe masu sukar lamirin shugaban.

Daruruwan mutane sun yi sun hadu a babban birnin kasar dauke da hotunan ‘yan hamayya, da ‘yan jarida da ‘yan raji da aka kama aka kulle.

Kungiyoyin kare hakkin bil Adama sun ce Saied ya kawar da ‘yancin walwala a kasar Tunisiya, ya maida kasar baki dayanta tamkar kurkuku, tun lokacin da ya ba ma kansa ikon gudanar da komai ta hanyar yin mulki bisa umurninsa shi kadai a shekarar 2021.

Siyasa

Post navigation

Previous Post: An Kashe Sojojin Bangladesh A Kasar Sudan
Next Post: PDP Zata Karbi Mulki 2027 Inji Shugabannin Jam’iyar

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu Yafara Wasu Dabaru Domin Samun Kuri’u Siyasa
PDP Zata Karbi Mulki 2027 Inji Shugabannin Jam’iyar Siyasa
Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
Mulkin Kama Karya Yazo Karshe a Kasar Bulgaria Siyasa
Kirana Ga ‘Yan Siyasar Arewa, Su Jira Sai 2031- Akume Labarai
Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • NLC Ta Yabawa Gwamnan Gombe Inuwa Yahaya
  • Jirgin Sama Ya Fadi A Kano
  • Shugaba Tinubu Ya Yayi Magana Game Da Kafa ‘Yan Sandan Jihohi
  • Tinubu Yafara Wasu Dabaru Domin Samun Kuri’u
  • Sojoji Sun Farmaki ‘Yan Ta’adda A Borno

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Tayi Barazanar Rage Tallafinta Wa Sudan Ta Kudu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Murkushe Wani Yunkurin Juyin Mulki A Jamhuriyar Benin Afrika
  • Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Guinea Bissau Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hukumar Tsaro Ta DSS Ta Aika Sammaci Dr. Yusuf Baba-Ahmed Labarai
  • Allah Ya Yi Wa Sheikh Dahiru Bauchi Rasuwa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump: Zamu Kawo Zaman Lafiya A Fadin Duniya Amurka
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Masu Garkuwar da Mutane a Jihar Gombe Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.