Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Tayi Barazanar Zata Rage Tallafin Da Take BayarwaSudan Ta Kudu, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai

An Gudanar Da Zanga-Zanga A Guinea-Bissau
Published: December 12, 2025 at 8:05 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 12, 2025

Daruruwan mutane sun yi macin yau jumma’a a titunan babban birnin Guinea-Bissau, domin nuna rashin jin dadinsu da juyin mulkin da aka yi a watan da ya shige, tare da neman a sako shugabannin hamayya da aka kama aka tsare.

Masu zanga zanga sun yi arangama da dakarun tsaro a Bissau a yayin da suka toshe hanyoyi ta hanyar kona tayu da kuma yin kiran da a sako Domingos Pereira, shugaban jam’iyyar hamayya wanda aka kama a lokacin juyin mulkin.

Hafsoshin soja sun hambarar da shugaba Umaero Sissoco Embalo a ranar 26 ga watan nuwamba, kwana daya kafin hukumar zabe ta kasar ta bayyana sakamakon zaben shugaban kasar da aka yi.

Sojojin sun nada manjo janar Horta Inta-a a matsayin shugaban kasar na wucin gadi.

A yayin da wannan ke faruwa ne kuma shugabannin kungiyar tarayyar tattalin arzikin kasashen yankin na Afirka ta yamma, ECOWAS, suke shirin ganawa a Abuja, babban birnin tarayyar Naeriya domin tattauna lamarin na kasar Ginea-Bissau, tare da nazarin kafa mata takunkumi.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Messi Da Cristiano Suna Da Tasiri A Gasar Cin Kofin Duniya 2026
Next Post: Akalla Mutane 8 Sun Mutu Biyo Bayan Bindiga Da Wata Tanka Tayi

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Ta Gabatarwa Sassan Dake Yakar Juna A Sudan da Shirin Tsagaita Wuta Afrika
Sojojin Da Suka Kifar Da Farar Hula A Guinea-Bissau Sun Sanar Da Cewa! Afrika
Najeriya Ta Bawa Dan Takarar Guinea-Bissau Mafaka Afrika
An Damke Matasa Masu Gurza Kudaden Ketare Na Jabu Afrika
ECOWAS Ta Saka Dokar Ta Baci A Afrika Ta Yamma Afrika
Gwamnatin Soji A Nijar Ta Hana Fitar Da Albarkatun Kasa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Anyi Jefe-Jefe Yayin Rangadin Messi, A Indiya
  • Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano
  • Gidauniya: An Fara Tiyatar ‘Hernia’ Da ‘Hydrocele’ Kyauta A Jihar Katsina
  • Amurka Ta Daina Bawa Israila Bayanan Sirri
  • Kasashen Cambvodia Da Thailand Sun Kulla Yarjejeniyar Tsagaita Wuta

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Tinubu: Sojojin Mu Sun Yi Rawar Gani Don Kare Demokuraɗiyya A Jamhuriyar Binin Labarai
  • Trump Da Bin Salman Da Wasu Kasashe Za Su Sa Hannu A Rikicin Sudan Labarai
  • Yajin Aikin Ma’aikatan Lafiya Na Shafar Harkokin Jinya A Asibitoci Kiwon Lafiya
  • Ruwan Sama Ya Dai-Daita ‘Yan Gudun Hijira A Gaza Labarai
  • IBB: Ba Shakka Abiola Ya Lashe Zaben Yuni 12 Rediyo
  • Sojojin Amurka Sun Kashe Wasu Fararen Hula Ba Dalili Amurka
  • CAN: Da Alamu Daliban St. Mery Na Cikin Koshin Lafiya Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.