Gwamnan jihar Kebbi Dr. Nasir Idris (Kauran Gwandu), ya amince da biyan kudaden garatuti da tallafin rasuwa ga ma’aikatan gwamnati da suka yi ritaya da kuma wadanda suka rasu, da ma’aikatan kwantiragi, ma’aikatan kananan hukumomi da kuma na Hukumar Ilimin Kananan Hukumomi.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Shugaban Ma’aikatan jihar Malami Shekare mni, ya fitar wadda Daraktan Gudanarwa, Rashidu Muhammad Bala FCIA, FCIHRSM, ya sanya wa hannu.
Sanarwar ta bayyana cewa amincewar ta shafi kashi biyu na biyan kudaden.
Kashi na farko ya shafi daga 16 ga watan Maris zuwa 15 ga Yuni, 2025, inda aka biya jimillar kudi Naira ₦933,028,860.33 ga mutum 404.
Kashi na biyu kuwa ya shafi daga 16 ga Yuni zuwa 15 ga Satumba, 2025, inda aka biya jimillar kudi Naira ₦932,948,801.39 ga mutane 443.
Biyan wadannan hakkoki na nuna jajircewar gwamnatin Nasir Idris wajen kula da walwalar ma’aikata da iyalan wadanda suka rasu, tare da kudurinta na rage basussukan da ake bin gwamnati a bangaren ayyuka.


