Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Kano: Zamu Kara Daukar Malamai Domin Inganta Ilimi
Published: December 11, 2025 at 10:54 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Kano za ta dauki sabbin malaman makaranta dubu hudu a fadin jihar.

Shugaban Hukumar Ilimi Matakin Farko a jihar, (SUBEB), Yusuf Kabir, ya ce hukumar na shirin daukar karin malamai dubu hudu domin karfafa koyar da karatu a Matakin farko da lissafi a kananan hukumomin jihar.

Ya bayyana hakan ne a taron bitar sakamakon karatun dalibai na ƙarshen shekarar 2025, wanda aka shirya domin tattaunawa da masu ruwa da tsaki kan ci gaban koyon ilimi a karkashin shirin Partnership for Learning for All in Nigeria (PLANE) na tsawon shekaru uku, wanda gwamnatin Birtaniya ke tallafawa.

Kabir, wanda sakatariyar hukumar, Hajiya Amina Umar, ta wakilta, ya bayyana cewa duk da cewa malamai 4,343 aka dauka a karin daukar ma’aikatan baya-bayan nan, amma har yanzu jihar na fama da karancin malamai.

A cikin sabbin gyare-gyaren da ake shirin aiwatarwa, jihar na kokarin rage cunkoson aji daga tsarin malami daya kan dalibai 132 a wasu ajujuwa zuwa burin samun malami daya kan dalibai 60.

Wani mai ruwa da tsaki, Dr. Miswaru Bello, ya bayyana damuwa cewa kashi 40% na daliban Kano ba sa halartar aji, yayin da rashin halartar malamai ke kaiwa kusan kashi 12%.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Kasar Iceland Ta Kauracewa Bikin Gasar Wakokin Shekara Mai Zuwa
Next Post: Mace Ta Farko Da Zata Shugabanci Jami’ar Northwest Dake Kano

Karin Labarai Masu Alaka

Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas Najeriya
Masu Ruwa da Tsaki akan Lamurran Siyasa sun Fara Maida Martani akan Matakin da Ministan Labaran Nigeria da wayar da kan Jama,a Idris Malagi na korar Daya Daga cikin Ma,aikatansa Saboda dalilai na Siyasa. da tsakiayar ranar Wannan larabace dai Mataimakin na Musamman akan yada Labarai ga Minista Malagi Malam Rani,u Ibrahim ya fitar da Wata sanarwar cewa Ministan ya Dakatar da Daya Daga cikin Ma,aikatansa Mai Suna Sa,idu Enagi Saboda ya fitar da Wani bayani a Kafar yada Labarai na sada zumunta dake Nuna Ministan ya shirya tsaf Domin takarar Gwamnan Jihar Neja a 2027. Malam Sa,idu Etsu Tsohon Dantakarar Shugaban cin Jam,iyyar APC a Nigeria Yace Matakin da Ministan ya Dauka yayi Dai dai Domin yanzu lokaci baiyi ba..ceu.. Shima Dattijon Siyasa a Jihar Neja Alh.Awaisu Giwa Kuta Yace Matakin da Ministan Labaran ya Dauka yayi Dai dai Domin yanzu Jihar Neja zaman Makoki Ake na fotinar Yan ta,adda ba wai Batun Neman Mukamin Siyasa ba..ceu .in.. To Sai jigon Jam,iyyar PDP Mai Adawa a Nigeria Hon.Yahaya Ability Yace Akwai kuskure Babba da Ministan ya tabka a dai dai Wannan Zamani na Siyasa duk da cewa Jihar Nejan na cikin Yanayi na masifar Yanbindiga..ceu..in .. Azaben Shekara ta 2023 Malagi ya kara yayi Takara Gwamnan Jihar Neja a jam,iyyar APC inda Gwamna Umar Bago ya kadashi a zaben fidda Gwani. Martanin Wasu ‘Yan Najeriya Ga Ministan Labarai Bisa Korar Dadiminsa Najeriya
Jakadan Kasar Sin a Najeriya Ya Ziyarci Tinubu Najeriya
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Zuwa Jami’ar Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Bola Ahmed Tinubu Ya Soke Bashin Da Gwamnati Take Bin NNPC Najeriya
Shugaba Tinubu Ya Turawa Majalisa Sunayen Mutane Biyun Da Zasu Shugabanci Sashin Albarkatun Mai Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Muna Kokarin Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Gombe – Uwargidan Gwamna
  • Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet
  • Yeriman Ingila Ya Gana Da Yeriman Saudiya Mai Jiran Gado
  • Dubban Mutane Sunyi Zanga-Zanga A Kasar Australia
  • Bangladesh Tasamu Rangwamen Harajin Da Amurka Ta Kakaba Mata

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Shugaban Kasar Uganda Yana Kokarin Mayar Da Mulkin Kasar Na Gado Labarai
  • Kasar Amurka Takara Saka Takunkumi Akan Kasar Venezuela Amurka
  • CAF Ta Fara Binciken Rikicin Bayan Wasa Tsakanin Algeria Da Najeriya Wasanni
  • Shugaba Trump Ya Amince Da Tsawaita Cinikayya Tsakanin Amurka Da Kasashen Afirka Afrika
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Litinin 11.17.2025 Rediyo
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Daruruwan Mutane A Afirka Ta Kudu Afrika
  • Nuhu Ribadu Ya Mika Dalibai 100 da Aka Ceto Ga Gwamnatin Jihar Neja Labarai
  • NUJ: Akwai Bukatar Inganta Albashin ‘Yan Jarida A Najeriya Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.