Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Kasar Amurka Takara Saka Takunkumi Akan Kasar Venezuela
Published: December 12, 2025 at 7:41 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

A ranar Alhamis, kasar Amurka ta saka sabbin takunkumi kan kasar Venezuela, inda ta kafa doka kan ‘yan uwan uwargidan shugaba Nicolas Maduro su uku da kuma takunkumi kan tankokin dakon mai da kamfanonin dake da alaka da su, yayin da Amurkan ke ci gaba da matsin lamba ga Caracas, fadar shugabancin Venezuela.

Daukan matakin ya biyo bayan da Amurka ta girke dakarun soja da dama yankin na kudancin karibiyan, kuma yayin da shugaba Doald Trump ke yakin neman hambarar da Maduro. Trump ya ce Amurka ta kame wani jirgin dakon mai da aka sawa takunkumi a gabar kogin Venezuela.

A wata sanarwa sashen kula da baitul malin Amurka, ta ce ta kakaba takunkumi kan kamfanoni 6 masu dakon man Venezuela, da kuma wasu tankokin dakon mai su shida, wanda ta ce suna aikata magudi, da matakan da zasu iya cutarwa, kuma suna ci gaba da samar da kudade da ke taimakawa mulkin Maduro na magudi da ta’addanci.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Yanayin Sanyi Yayi Kamari a Yankin Gaza
Next Post: Mulkin Kama Karya Yazo Karshe a Kasar Bulgaria

Karin Labarai Masu Alaka

Kadan Daga Cikin Abubuwan Da Suka Faru A 2025 A Nan Amurka Amurka
Kasuwannin Hannayen Jari Suna Fuskantar Durkushewa Sakamakon Matsin Lambar Shugaba Trump Amurka
Shugaba Putin Ya Bukaci Kawo Karshen Yaki Da Iran Afrika
Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka Ta Saka Takunkumi Visa Ga Wasu ‘Yan Rwanda Afrika
Emmanuel Macron: Yakamata Wani Sashi Ya Rika Takawa Wani Sashi Birki A Tsarin Demokradiya Amurka Amurka
Rahoton Leken Asiri Yanuna Cewa Harin Amurka Bazai Samar Da Shugabanci A Iran Ba Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojoji Zasu Taimakawa ‘Yan Sanda Wajen Yaki Da Mugayen Ayyuka Labarai
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe ‘Yan Sanda A Jihar Katsina Najeriya
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojin Najeriya Da ‘Yan Ta’adda Sunyi Taho Mugama Najeriya
  • Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta Duniya Zata Binciki Kasar Iran Afrika
  • Yanbindiga sun Kashe kimanin mutane 30 a yankin kayama ta Jihar kwaran Najeriya Najeriya
  • Tinubu Ya Yi Allah Wadai Da Kashe-kashen Jos Da Kaduna Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.