Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Amurka Tayi Barazanar Zata Rage Tallafin Da Take BayarwaSudan Ta Kudu, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

An Shirya Taron Horas Da Matasa Gabanin Wasan Motsa Jiki 2025
Published: December 6, 2025 at 11:32 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 7, 2025

An shirya taron kara wa juna sani na kwana daya don tunkarar wasannin Motsa jiki a Jihar Bauchi.

Ma’aikatar Matasa da Wasanni na jihar Bauchi a tarayyar Najeriya,ta shirya taron bita don kara wa juna Ilimi kan wasannin Motsa jiki na Matasa karo na hudu, da zai gudana a Jihar Bauchi.

Kwamishinan Ma’aikatar Matasa da Wasanni Hon Babayo Adamu Gabarin, wadda ya samu wakilcin mai rikon Babban Sakatare a ma’aikatar Alh Abdullahi Ibrahim ya bayyana maka sudin shiya wannan taron.

Ya ce an shirya bitanne wa Jagororin Wasanni (Sport Officer) da suke kananan hukumomi ashirin dake fadin jihar Bauchi don sani ka’idoji da kuma yadda za’a ciyar da Bauchi gaba ta fanin wasannin.

Cikin bayanin sa Kwamishinan yace ya zamo dole su tabbatar da cewa sun debo ‘yan wasa na jiha banda dauko wasu a wajen jiha, ya kuma jadda aniyar gwamnati na basu goyan baya yakara da bayyana muhimmancin shirya wannan gasa shine don a samu a zakulo yara masu hazaka wa ‘yanda zasu wakilci jiha a wasannin Kasa.

Kwamishinan yace saboda maigirma Gwamnan Bauchi Bala Abdulkadir Muhammad yayi dukkanin abunda ya dace wa bangaren Matasa da Wasanni a jiha kuma ya dukufa wajan gyara da kuma gina sabbin wajan wasanni a fadin jihar Bauchi wacce ake mata ta ke da (Mecca of Sport).

An ja hankalin mahalarta taron da su bi dokokin Gasar dan kauce wa hukunci yayin wannan wasa da za’ayi shi ranar 13 ga watan Disamba a kuma rufe 20 ga watan 10/ 2025, kwanaki bakwai kinan.

Mun samar da dukkanin kayayakin da ake bukata don ganin gasar ya tafi kamar yadda aka tsara ” in ji shi.

Kananan hukumomi ashirin ne da suke fadin jihar Bauchi zasu halarci wannan gasa inda za’ayi Wasanni kala-kala har sama da ashirin da suka shafi guje-guje tsale-tsale kokawa, to kwallon kwando, damben zamani da ma sauran wasannin irin zamani ciki harda wasannin gargaji irin su langa.

Wasannin ya kunshi bangaren Maza da Mata da ma bangaren masu bukata ta musamman wato (Para Soccer).

Manyan baki da suka halarci wannan taron sun hada da tsaffin Daraktoci a Hukumar wasanni na jihar Bauchi, da wadda ya ke kai da Shugaban Hukumar Alh Ado Amah, da wasu Jagororin gidan bangaren Mata inda dukkanin su suka bada lakca kan yadda za’a tun kari gasar cikin sauki.

Daya daga cikin mahalarta taron Abdulmalik Aminu wadda shine jami’in wasanni na karamar hukumar Bauchi, kuma Shugaban jami’ai na wasani a jiha, ya bayyana farin cikinsa da wannan taron horaswan inda yace zasuyi anfani da abunda a ka koya musu da zaran sun koma wajan aikinsu don zakulu hazikan yara da zasu fafata a gasar kuma su wakilci jiha a matakin tarayyar.

Ya kuma gode wa ma’aikatar Matasa da Wasanni na jihar Bauchi karkashin Hon Babayo Adamu Gabarin, da sukayi wannan tunani na kara wa juna sani. Yayin wannan taro an raba wa mahalarta taron takardar shaidan halartan horaswar (Certificate).

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Jirgin Sojin Saman Najeriya Yayi Hatsari a Jihar Neja
Next Post: Hukumar CAC Zata Dakatar da POS Mara Rijista a Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

An Bude Gasar Kwallon Kafa Ta Mata A Najeriya NWFL 2025 Wasanni
Kocin Ranchers Bees Ya Yi Murabus Wasanni
FIFA, Ta Raba Jaddawalin Rukuni Na Gasar Kofin Duniya 2026. Wasanni
CAF, Zata Ci Tarar Wasu Kasashe AFCON 2025 Wasanni
Da Alamu Ronaldo Zai Buga Dukkan Wasanni Da Gasar Kofin Duniya A 2026 Wasanni
Kocin Zambia Na Mata Ba Lafiya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike a Tituna
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakuncin Wasannin Afirka Na 2031.
  • Mulkin Kama Karya Yazo Karshe a Kasar Bulgaria

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Magoya Bayan Nice Sun Kai Hari Wa ‘Yan Wasansu Wasanni
  • Kasashe 5 Da Ke Fama Da Matsanancin Zazzabin Cizon Sauro Rediyo
  • “Banga Abun Da Zai Canza Ba A Nadin Janar Christopher Ministan Tsaro” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gobara Mafi Muni Cikin Shekaru 60 A Hong Kong Ta Hallaka Rayuka Sauran Duniya
  • Rikici Tsakanin NNPC Da Kungiyar Gwamnoni Akan Gibin Kudade Labarai
  • An Murkushe Wani Yunkurin Juyin Mulki A Jamhuriyar Benin Afrika
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Alhamis 11.20.2025 Rediyo
  • An Damke Wani Likita Da Ke Taimakawa ‘Yan-Ta’adda Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.