Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Majalisar Wakilai Ta Rikon Kwaryar Nijar Ta Gudanar Da Zama Karo Na Biyu
Published: December 17, 2025 at 3:05 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Majalissar wakilai ta rikon kwaryar jamhuriyar Nijar ta fara zamanta na biyu na karshe a shekarar nan ta 2025.
A tsawon kwanaki biyu na wannan zama wakilan zasu tattauna batutuwa da dama da suka shafi tafiyar kasar kamar yadda  gwamnatin mulkin sojan kasar ta shigar da bukata. Sai dai wasu ‘yan kasar sun shawarci majalissar a kan wasu karin batutuwan da ke bukatar matakan gaggawa.
 Taron Wanda ke matsayin na rufe shekarar nan ta 2025 lokaci ne da wakilai 194 na majalissar ta conseil consultatif de la refondation zasu nazarci kudirorin da gwamnatin ta Nijar ta zo da su da suka shafi fannoni da dama.
Farfesa Dicko Abdourahamane na daga cikin mahalarta taron.
Kundin tsarin mulkin gwamnatin ta rikon kwarya da ya samo asali daga babban taron rukunonin al’ummar kasar ya bai wa majalissar hurumin sauraren mimbobin gwamnati idan bukatar hakan ta taso saboda haka a wannan karon za su mori wannan dama kamar yadda shugaban kwamitin kula da siyasar duniya a majalissar CCR Bana Ibrahim ya bayyana.
Duk da cewa zaman na da mahimmanci a wajensu wasu ‘yan Nijar kamar su Salissou Ibrahim na FRSA na jan hankula a kula da wasu abubuwan da a cewarsa suna kan gaba a jerin manufofin shugaban kasa.
Shi kuma shugaban kungiyar yaki da cin hanci ta RENAC kwararre kan sha”anin shugabanci Adamou Oumarou na kokarin ankarar da zaman na wannan karon kan matakan taka birki daga yunkurin ciyo bashi daga waje.
A karshen taron na kwanaki 15 majalissar ta CCR za ta gabatar da takardun shawarwari wa bangaren zartarwa inda Janar Abdourahamane Tiani da ke da maganar karshe zai yi na’am kokuma ya bukaci majalissar ta yi Zaman gaggawa don kwaskware abinda ke bukatar gyara.
TARON MAJALISSAR WAKILAI
Afrika

Post navigation

Previous Post: Cutar Zazzabin Lassa Tayi Ajalin Mutum 1 Yayinda Mutane 11 Suka Kamu A Jihar Gombe
Next Post: Jirgin Ya Fado Ne Da Maraice Kuma Ya Taso Daga Kaduna Zuwa Fatakol Sai Aka Sauya Masa Hanyar Zuwa Owerri

Karin Labarai Masu Alaka

ECOWAS Ta Saka Dokar Ta Baci A Afrika Ta Yamma Afrika
Kasar Congo Ta Dau Alwashin Bin Tsari Wajen Rarraba Ma’adanai Afrika
‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery Afrika
Akalla Mutane 8 Sun Mutu Biyo Bayan Bindiga Da Wata Tanka Tayi Afrika
Najeriya Ta Bawa Dan Takarar Guinea-Bissau Mafaka Afrika
Nijar: Zamu Tsananta Bincike A Bakin Iyakokin Mu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Fintiri: Zamu Maida Jihar Adamawa Sabuwar Duniya
  • Gwamnatin Najeriya Ta Dauki Matakai Don Farfaɗo Da Maɗaba’ar Gwamnati
  • Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno
  • A Kowacce Rana Kasar China Tana Sayan Danyen Mai Ganga Dubu 600 Daga Kasar Venezuela
  • Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Maharan Bindiga Sun Kashe Mutane 12 Masu Hakar Ma’adanai A Jihar Filato Labarai
  • Jakadan Kasar Sin a Najeriya Ya Ziyarci Tinubu Najeriya
  • Ana Cigaba Da Kai Kayan Agaji Kasar Morocco Sakamakon Tsananin Hunturu Afrika
  • Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Roger Lumbala Shekaru 30 Labarai
  • Amurka Ta Kama Wani Jirgin Dakon Mai Amurka
  • Dangote Ya Rage Farashin Mai A Najeriya Labarai
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 15 A Kasar Australiya Labarai
  • Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Guinea Bissau Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.