Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Majalisar Wakilai Ta Rikon Kwaryar Nijar Ta Gudanar Da Zama Karo Na Biyu
Published: December 17, 2025 at 3:05 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Majalissar wakilai ta rikon kwaryar jamhuriyar Nijar ta fara zamanta na biyu na karshe a shekarar nan ta 2025.
A tsawon kwanaki biyu na wannan zama wakilan zasu tattauna batutuwa da dama da suka shafi tafiyar kasar kamar yadda  gwamnatin mulkin sojan kasar ta shigar da bukata. Sai dai wasu ‘yan kasar sun shawarci majalissar a kan wasu karin batutuwan da ke bukatar matakan gaggawa.
 Taron Wanda ke matsayin na rufe shekarar nan ta 2025 lokaci ne da wakilai 194 na majalissar ta conseil consultatif de la refondation zasu nazarci kudirorin da gwamnatin ta Nijar ta zo da su da suka shafi fannoni da dama.
Farfesa Dicko Abdourahamane na daga cikin mahalarta taron.
Kundin tsarin mulkin gwamnatin ta rikon kwarya da ya samo asali daga babban taron rukunonin al’ummar kasar ya bai wa majalissar hurumin sauraren mimbobin gwamnati idan bukatar hakan ta taso saboda haka a wannan karon za su mori wannan dama kamar yadda shugaban kwamitin kula da siyasar duniya a majalissar CCR Bana Ibrahim ya bayyana.
Duk da cewa zaman na da mahimmanci a wajensu wasu ‘yan Nijar kamar su Salissou Ibrahim na FRSA na jan hankula a kula da wasu abubuwan da a cewarsa suna kan gaba a jerin manufofin shugaban kasa.
Shi kuma shugaban kungiyar yaki da cin hanci ta RENAC kwararre kan sha”anin shugabanci Adamou Oumarou na kokarin ankarar da zaman na wannan karon kan matakan taka birki daga yunkurin ciyo bashi daga waje.
A karshen taron na kwanaki 15 majalissar ta CCR za ta gabatar da takardun shawarwari wa bangaren zartarwa inda Janar Abdourahamane Tiani da ke da maganar karshe zai yi na’am kokuma ya bukaci majalissar ta yi Zaman gaggawa don kwaskware abinda ke bukatar gyara.
TARON MAJALISSAR WAKILAI
Afrika

Post navigation

Previous Post: Cutar Zazzabin Lassa Tayi Ajalin Mutum 1 Yayinda Mutane 11 Suka Kamu A Jihar Gombe
Next Post: Wani Jirgi Yayi Saukar Angulu Ba Shiri

Karin Labarai Masu Alaka

Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi Afrika
Wani Alkali A Amurka Ya Kalubalanci Gwamnatin Kasar Afrika
Sanyin Hunturu Yayi Ajalin ‘Yan Cirani A Morocco Afrika
Iran Zata Shigar Da Lebanon Cikin Cimma Yarjejeniya Afrika
Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda Afrika
Ministan Harkokin Wajen Iran Yagana Da Shugaban Sa’ido Akan Nukiliya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnan Gombe Ya kori Wasu Hadimansa Bisa Cin Zarafin Kansila Najeriya
  • Makarantun Allo Zasu Yi Gogayya Da Na Boko Labarai
  • Akwai Bukatar Bincikar Umurnin Da Sakataren Tsaro Pete Ya Bada Amurka
  • Kasar Saudiya Zatayi Gwajin Noman Dabino A Kano Labarai
  • Gwamnonin Arewa “Mun Amince Da Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaban Rasha Yafara Ganawa Da Jakadun Amurka Domin Kawo Karshen Yakin Ukraine Amurka
  • Kasar China Ta Sauka Daga Ragamar Bada Bashi Labarai
  • Duniyar Dambe A Makon Jiya Nishadi
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.