Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Amurka Tayi Barazanar Zata Rage Tallafin Da Take BayarwaSudan Ta Kudu, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Ribadu: Najeriya Ce Kasa Daya Tilo Da Ke Tabbatar Da Demokraɗiyya A Sahel
Published: December 4, 2025 at 8:58 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Mai bawa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro (NSA), Nuhu Ribadu, ya gargadi cewa dole ne a kare tsarin dimokraɗiyyar Najeriya, kasancewarta kasa daya tilo da take aiwatar da demokraɗiyya a duk yankin Sahel, inda rikice rikicen siyasa da juyin mulki suka yi kamari.

Ribadu ya yi wannan jawabi ne a Abuja, a wani taron tattaunawa kan rigakafi wanda Kwamitin Zaman Lafiyar Kasar, Cibiyar Kukah da Ofishin Mai bawa shugaban kasa shawara ta bangaren tsaro suka shirya.

Wannan gargadi nasa ya zo ne a daidai lokacin da juyin mulki ya yi katutu a kasashen yammacin Afirka da Sahel, kamar su Mali, Burkina Faso, Nijar da Chadi, inda aka sami hambarar da gwamnatoci.

Ribadu ya ce duk da kalubalen tsaro da na tattalin arziki da Najeriya ke fama da su, ita ce kadai kasa a yankin da har yanzu ke gudanar da mulkin farar hula bisa kundin tsarin mulki.

Ya kuma bayyana cewa gwamnatin Najeriya ta samu hukuncin laifi 775 a kan masu aikata ta’addanci abin da ya ce alama ce ta ci gaban da ake samu sakamakon hadin kan hukumomin tsaro, al’umma da kuma bangaren shari’a.

Sai dai ya jaddada cewa wadannan nasarori na iya rushewa idan rikici, tashin hankali da rabuwar kai suka ci gaba da yawaita.

Ribadu ya kara da cewa ana iya samun zaman lafiya mai dorewa ne kawai idan tattaunawa ta rikide zuwa matakai na zahiri da za su kara karfin garkuwar al’umma, su dawo da amana, su kuma inganta tsaro a arewacin Najeriya.

Ya bayyana cewa yawancin matsalolin tsaro a kasa sukan fara ne daga matakin ƙananan hukumomi, yana mai jaddada muhimmancin rawar da al’umma, sarakunan gargajiya, malamai da gwamnatocin jihohi ke takawa wajen dakile rikici ya jadda da cewa idan aka bai wa al’umma damar magance matsalolinsu da kansu, buƙatar tura dakarun soja tana raguwa ƙwarai.

A nasa bangaren, shugaban kwamitin zaman lafiya na kasa, Bishop Matthew Kukah, ya ce matsalar tsaro ta taba kusan kowane dan Najeriya kai tsaye.

Bishop Kukah ya yi watsi da ra’ayin cewa al’umma su dauki makamai domin kare kansu, yana mai cewa daukar makami ba ya kawo tsaro na gaskiya, illa zai haifar da sabbin matsaloli a kasar.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Christ Musa Ministan Tsaro
Next Post: Kyaftin Na Super Eagles Ya Yi Ritaya.

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Christ Musa Ministan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaba Tinubu Ya Umurci Janyewa Manyan Mutane ‘Yan Sanda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kotun Tarayya Ta Yankewa Nnamdi Kanu Daurin Rai-da-Rai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Ya Zamo Khalifan Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Kasar Benin Ta Nemi ‘Yan Kasa Su Kwantar Da Hankali Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ana Cigaba Da Jimamin Rasuwar Mataimakin Gwamnan Bayelsa
  • Bahagon Mancha Ya Buge Bahagon Maitakwasara Da Wasun Su!
  • Shirin Manuniya Yau Juma’a 12.12.2026
  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike A Tituna
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Juma’a 11.21.2025 Rediyo
  • Ruwan Sama Ya Dai-Daita ‘Yan Gudun Hijira A Gaza Labarai
  • Sojojin Da Suka Kifar Da Farar Hula A Guinea-Bissau Sun Sanar Da Cewa! Afrika
  • Tsohon Minista Ngige Ya Shiga Komar EFCC Najeriya
  • Abun Da Kuke Buƙatar Sani Game Da Gasar Cin Kofin Ƙasashen Afirka 2025 Wasanni
  • Chelsea Tayi Kaca-Kaca Da Barcelona A Gasar UCL Wasanni
  • Guterres: Babban Kuskure Ne Yadda Isra’ila Ta Kai Farmaki A Gaza Labarai
  • Jiragen Saman Yakin Najeriya Suka Gurgunta Yunkurin Juyin Mulki A Benin Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.