Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Yau Litinin Za’a Mika Daliban Ga Iyayen Su
Published: December 22, 2025 at 5:06 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kakakin shugaba Bola Ahmed Tinubu na Najeriya, yace an sako sauran dalibai 130 da aka sace daga wata makaranta ta ‘yan Katolika a jihar Neja, daya daga cikin sace-sacen mutane mafi muni da aka gani a kasar cikin ‘yan shekarun nan.

Bayo Onanuga ya fada cikin wata sanarwar da ya fitar a shafin X cewa an sako sauran dalibai 130 da ‘yan ta’adda suka sace, yana mai fadin cewa a yau litinin ake sa ran zasu isa Minna, babban birnin Jihar Neja, kuma zasu koma cikin ‘yan’uwansu domin suyi bukukuwan kirsimeti tare.

Mr. Onanuga yace daliban su samu ‘yan cinsu ne a bayan wani mataki na soja da jami’an leken asiri.

Daliban suna daga cikin yara fiye da 300 da malamai 12 da ‘yan bindiga suka sace daga makarantar St Marys Catholic dake garin Papiri da asubahin ran 21 ga waran Nuwamba.

Sace daliban ya haddasa fusata kan yadda rashin tsaro yake kara yin muni a yankin arewacin Najeriya, inda ‘yan bindiga ke kai hare-hare kan kauyuka da garuruwa da ma makarantu suna sace mutane don neman a biya su kudin fansa.

Labarai

Post navigation

Previous Post: An Sako Ɗaliban Makaranta 130 Da Aka Sace A Jihar Neja 
Next Post: Hari Akan Wata Mashaya Ya Rutsa Da Mutane 9 A Afirka Ta Kudu

Karin Labarai Masu Alaka

Jami’an Diflomasiyyar Iran Dana Amurka Sun Tattauna A Kasar Oman Afrika
Angano Gawar Wani Dan Myanmar A Arewacin New York Afrika
Gwamna Inuwa Yahaya ya Rusa Majalisar Zantaswa ta Jihar Gombe Labarai
Mizanin Tattalin Arzikin Najeriya Na 2024 Ya Karu Da Kashi 3.84% Labarai
Dangote Ya Rage Farashin Mai A Najeriya Labarai
Shugaban Amurka Yayi Barazanar Kulle Wani Dan Jarida Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
  • Chelsea Tayi Kaca-Kaca Da Barcelona A Gasar UCL Wasanni
  • Ana Gudanar Da Zaben Shugaban Kasa A Djibouti Yau Juma’a Afrika
  • Shugaban Amurka Yace Sojojin Amurka Dana Iran Sunyi Taho Mugama Amurka
  • Kasar Ukraine Tayi Watsi Da Shiga Kungiyar NATO Labarai
  • Kotu A Najeriya Ta Kame Mutane Bisa Zargin Ta’addaci Afrika
  • Hukumar Kare Hakkin ‘Yan Jarida Tace Isra’ila Ce Ta Kashe ‘Yan Jarida Kashi Biyu Bisa Uku Labarai
  • Thailand Da Cambodia Sun Fara Tattauunawa Kan Batun Tsagaita Wuta Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.