Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Yau Litinin Za’a Mika Daliban Ga Iyayen Su
Published: December 22, 2025 at 5:06 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kakakin shugaba Bola Ahmed Tinubu na Najeriya, yace an sako sauran dalibai 130 da aka sace daga wata makaranta ta ‘yan Katolika a jihar Neja, daya daga cikin sace-sacen mutane mafi muni da aka gani a kasar cikin ‘yan shekarun nan.

Bayo Onanuga ya fada cikin wata sanarwar da ya fitar a shafin X cewa an sako sauran dalibai 130 da ‘yan ta’adda suka sace, yana mai fadin cewa a yau litinin ake sa ran zasu isa Minna, babban birnin Jihar Neja, kuma zasu koma cikin ‘yan’uwansu domin suyi bukukuwan kirsimeti tare.

Mr. Onanuga yace daliban su samu ‘yan cinsu ne a bayan wani mataki na soja da jami’an leken asiri.

Daliban suna daga cikin yara fiye da 300 da malamai 12 da ‘yan bindiga suka sace daga makarantar St Marys Catholic dake garin Papiri da asubahin ran 21 ga waran Nuwamba.

Sace daliban ya haddasa fusata kan yadda rashin tsaro yake kara yin muni a yankin arewacin Najeriya, inda ‘yan bindiga ke kai hare-hare kan kauyuka da garuruwa da ma makarantu suna sace mutane don neman a biya su kudin fansa.

Labarai

Post navigation

Previous Post: An Sako Ɗaliban Makaranta 130 Da Aka Sace A Jihar Neja 
Next Post: Hari Akan Wata Mashaya Ya Rutsa Da Mutane 9 A Afirka Ta Kudu

Karin Labarai Masu Alaka

Guguwa Mai Karfi Ta Raunata Dubban Mutane A Madagascar Labarai
Jirgin Ruwan ‘Yan Gudun Hijira Ya Nitse Kogi A Tunisiya Labarai
Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Biyan Hakkokin Tsofin Ma’aikata 800 Labarai
Aminu Tambuwal Ya Fice Daga PDP Ya Koma ADC Afrika
Makarantun Allo Zasu Yi Gogayya Da Na Boko Labarai
Layin Raba Wutan Lantarki Na Najeriya Ya Fashe Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kamfanin Dangote Zai Sayo Na’urori Daga Kasar China Kimiya
  • Gwamna Zulum: Ya Bukaci Sojoji Su Cigaba Da Yakar Boko Haram Da ISWAP Labarai
  • Zaizayar Kasa Tayi Ajalin Mutane 200 A Kasar Congo Afrika
  • Kamfanin Mai Mallakar Saudiya Aramco Zai Sanja Hanyar Fitar Da Danyen Mai Labarai
  • Bankin Duniya Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Afirka Da Yankin Sahara Afrika
  • An Dakatar Da Daniel Bisa Zargin Fyade Wasanni
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakoncin Wasannin Afirka Na 2031 Wasanni
  • Kamfanin Hakar Ma’adanai Na Kasar Kanada Ya Cigaban Da Aikinsa Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.