Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Rundunar Tsaron Haɗin Gwiwa Ta Arewa Maso Gabas Ta Kashe Fiye Da ‘Yan Ta’adda 438
Published: December 28, 2025 at 6:14 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar Tsaron haɗin gwiwa ta Arewa maso Gabashin Najeriya, Operation Hadin Kai (OPHK), ta kashe ‘yan ta’adda 438 na Boko Haram da ISWAP cikin watanni bakwai.

Kwamandan rundunar OPHK a yankin Arewa maso Gabas, Sashi na daya, Manjo Janar Abdulsalam Abubakar, ne ya bayyana hakan a ranar Asabar yayin liyafar Kirsimeti da aka gudanar a Maiduguri, inda ya ce an gudanar da ayyukan ne tsakanin watan Mayu da Disamba.

Abubakar ya ce jami’an rundunar sun kuma ƙwato makamai iri-iri 254, na’urorin sadarwa na Starlink guda 300, tare da ceto fararen hula 366 daga maboyar ‘yan ta’adda daban-daban.

Ya ce, Mika wuya da ‘yan ta’adda 881 na JAS/ISWAP tare da iyalan su, na daga cikin manyan nasarorin da suka nuna ci gaban da aka samu.

Janar ɗin sojan ya ƙara da cewa bikin Kirsimeti ya zo dai dai da ayyukan rundunar na lokacin rani a yankin.

Abubakar ya danganta nasarorin da aka samu a ayyukan haɗin gwiwar bisa ga samun goyon baya daga Babban Hafsan Sojojin Ƙasan Najeriya.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Yau Lahadi Ake Gudanar Da Zabe A Kasar Myanmar
Next Post: Jamhuriyar Nijar Ta Fitar Da Doka Domin Kare ‘Yancin ‘Yan Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

Jami’an Tsaro A Jihar Borno Sun Kama ‘Yan Bindiga Labarai
Gwamna Bala Kauran Bauchi Ya Koma Jam’iyar APM Afrika
Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya Labarai
Dakarun Gwamnatin Kasar Sham Tayi Mamaya Zuwa Gabashin Kasar Labarai
‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji A Jihar Kebbi Afrika
Shugaba Tinubu Zai Kara Karbo Bashin Dala Miliyan 516 Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Laraba 11.19.2025 Rediyo
  • Jamhuriyar Nijar Ta Dakatar Da Bawa Amurkawa Visa Afrika
  • Kasar Spain Zata Bada Diyya Ga Iyalen Wadanda Da Suka Rasu A Hatsarin Jirgin Kasa Labarai
  • Iran Ta Rufe Sararin Samaniyar Ta Labarai
  • Hukumar Raya Birane Ta Rushe Gine-Ginen Da Suka Keta Dokokin Tsara Birane A Gombe Labarai
  • Iran Tace Dole A Tsagaita Wuta A Lebanon Kafun Fara Shawarwari Amurka
  • Wasu Mutane 15 Sun Rasa Rayukan Su A Gabashin Kwango Afrika
  • EFCC Ta Tsare Tsohon Minista Abubakar Malami Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.