Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Rundunar Tsaron Haɗin Gwiwa Ta Arewa Maso Gabas Ta Kashe Fiye Da ‘Yan Ta’adda 438
Published: December 28, 2025 at 6:14 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar Tsaron haɗin gwiwa ta Arewa maso Gabashin Najeriya, Operation Hadin Kai (OPHK), ta kashe ‘yan ta’adda 438 na Boko Haram da ISWAP cikin watanni bakwai.

Kwamandan rundunar OPHK a yankin Arewa maso Gabas, Sashi na daya, Manjo Janar Abdulsalam Abubakar, ne ya bayyana hakan a ranar Asabar yayin liyafar Kirsimeti da aka gudanar a Maiduguri, inda ya ce an gudanar da ayyukan ne tsakanin watan Mayu da Disamba.

Abubakar ya ce jami’an rundunar sun kuma ƙwato makamai iri-iri 254, na’urorin sadarwa na Starlink guda 300, tare da ceto fararen hula 366 daga maboyar ‘yan ta’adda daban-daban.

Ya ce, Mika wuya da ‘yan ta’adda 881 na JAS/ISWAP tare da iyalan su, na daga cikin manyan nasarorin da suka nuna ci gaban da aka samu.

Janar ɗin sojan ya ƙara da cewa bikin Kirsimeti ya zo dai dai da ayyukan rundunar na lokacin rani a yankin.

Abubakar ya danganta nasarorin da aka samu a ayyukan haɗin gwiwar bisa ga samun goyon baya daga Babban Hafsan Sojojin Ƙasan Najeriya.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Yau Lahadi Ake Gudanar Da Zabe A Kasar Myanmar
Next Post: Jamhuriyar Nijar Ta Fitar Da Doka Domin Kare ‘Yancin ‘Yan Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

An Kusa Kawo Karshen Matsalolin Tsaro A Jihar Filato Afrika
Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Jihar Filato Afrika
An Farmaki ‘Yan Bindiga Da Dama A Jihar Zamfara Labarai
Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Najeriya Ta Tabbatar Da Kyautata Rayuwar Mambobin ta Labarai
Jam’iyyar APC Ta Rantsar Da Sabbin Shugabanni a Jihar Neja Labarai
Guguwa Mai Karfi Ta Raunata Dubban Mutane A Madagascar Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana Afrika
  • Anyi Janazar ‘Yan Shi’a 33 Da Aka Kashe A Masallacin Juma’a Sauran Duniya
  • Jagoran Kwankwasiya A Najeriya Ya Koma Jam’iyar ADC Labarai
  • Najeriya Ta Kai Wasan Kusa Da Na Karshe A Wasan Dambe Na Matasan Afirka Wasanni
  • Shugaba Donald Trump Ya Bayyana Cewa Yana Cikin Masu Zaben Sabon Jagoran Iran Amurka
  • Jami’ar Tarayya A Gombe Ta Karyata Harin ‘Yan Bindiga Najeriya
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Asabar 11.15.2025 Rediyo
  • Iran Da Amurka Zasu Kulla Yarjejeniyar Nukiliya Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.