Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Shugaba Trump Yace Amurka Ce Zata Rika Gudanar Da Harkokin Kasar Venezuela
Published: January 5, 2026 at 5:26 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

A yayin da ake ci gaba da zaman kaka-ni-ka-yi a kasar Venezuela, shugabar wucin gadi Delcy Rodriguez, a yanzu ta maye gurbin babban abokin huldar siyasar ta, shugaba Nicolas Maduro, wanda sojojin Amurka suka kama a wani farmakin cikin dare da suka kai a kasar.

Tun shekarar 2018 Rodriguez take rike da kujerar mataimakiyar shugaba Maduro, tana mai kula da harkokin tattalin arzikin kasar da ya dogara kusan kacokan kan man fetur, tana jagiorancin hukumar leken asirin kasar, kuma ita ce magajiyar kujerar shugabanci.

Rodriguez tana daga cikin manyan jami’an gwamnatin shugaba Maduro wadanda a bisa dukkan alamu sune suke rike da madafun iko na Venezuela, duk da cewa shugaba Donald Trump na Amurka da jami’ansa sun ce zasu matsa ma gwamnatin ta lamba don ganin ta yi aiki da manufofinsu game da kasar mai arzikin man fetur.

A ranar asabar ne kotun kolin kasar ta umurce ta da ta karbi ragamar shugabancin kasar, inda kuma ta samu goyon bayan rundunar sojojin Venezuela.

A cikin jawabin da tayi ma kasar ta talebijin, Rodriguez ba ta nuna alamun cewa zata hada kai da shugaba Trump ba, tana mai bayyana gwamnatinsa a zaman ta ‘yan tsagera.

A yayin da manyan jami’an fararen hula da na soja suke kewaye da ita, Rodriguez ta ce shugaba guda daya kasar Venezuela take da shi, kuma shine shugaba Nicolas Maduro, ta ce abinda ake aikata ma kasar Venezuela, ta’asa ce wadda ta keta dokoki na kasa da kasa.

Rodriguez, lauya kuma ‘yar siyasa mai shekaru 56 da haihuwa, ta jima tana wakiltar akidar gurguzu da juyin juya halin da marigayi shugaba Hugo Chavez ya kafa a kasar.

A ranar asabar da safe, an yi mamaki da aka ji shugaba Trump yana cewa sakataren harkokin wajensa Marco Rubio yayi magana da Rodriguez, kuma ta yi godiya, sannan zata yi aiki da gwamnatin Amurka yayinda Rubio yace gwamnatin Amurka zata iya yin aiki tare da Rodriguez, ba kamar Maduro ba.

Ranar lahadi, lafazin shugaba Trump ya canja a yayin da Rodriguez da sauran jami’an gwamnatin Venezuela suka ci gaba da caccakar gwamnatin sa, tare da jaddada cewa sune suke rike da kasar ba Amurka ba.

A cikin wata hirar da yayi da jaridar The Atlantic, shugaba Trump yayi barazanar cewa idan har ba ta yi abinda ya kamata ba, to zata dandana kudarta ita ma, fiye ma da Maduro.

A ranar lahadin kuma Rubio yace ba ya daukar Rodriguez da gwamnatinta a matsayin halaltattu a saboda a cewarsa, kasar ba ta gudanar da zaben gaskiya ba.

A halin da ake ciki, sakataren harkokin wajen na Amurka Marco Rubio, yace Amurka ba zata dauki nauyin gudanar da harkokin mulkin yau da kullum na Venezuela ba, sai dai zata ci gaba da matsa lamba ta hanyar tabbatar da ci gaba da yin aiki da takunkumin mai da aka sanya ma kasar.

Wannan kuwa, babban juyi ne daga kalamen da shugaba Trump yayi kwana guda kafin nan inda yace Amurka ce zata rika gudanar da harkokin kasar ta Venezuela a bayan hambarar da Nicolas Maduro da kama shi.

Amurka, Labarai

Post navigation

Previous Post: Tinubu: Abba Magajin Aminu Kano Ne A Fagen Siyasa
Next Post: Koriya Ta Arewa Ta Gudanar Da Gwajin Makami Mai Linzami

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumar ‘Yan Sanda Ta Bukaci Jama’ar Jos Ta Arewa Su Rika Bin Doka Afrika
Majalisar Malaman Yarbawa Ta Yi Jimamin Rasuwar Babban Limamin Nuruddeen A Gombe Afrika
Birtaniya Ta Bukaci Israela Ta Janye Shawarar Fadada Iko Da Kogin Jordan Labarai
Ukraine Takai Hari Wajen Kera Makami Mai Linzami A Rasha Labarai
Gwamnatin Jihar Neja Ta Soke Lasisin Mallakar Wasu Manyan Filaye A Jihar Labarai
CP Chuso Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Gwiwar Hukumomin Tsaro A Gombe Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe ‘Yan Sanda A Jihar Katsina Najeriya
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojin Ukraine Sun Janye Daga Gabashin Kasar Amurka
  • Mace Ta Farko Da Zata Shugabanci Jami’ar Northwest Dake Kano Najeriya
  • Amy Hunt Ta Zama Sabuwar Tauraruwar Wasannin Guje-guje Ta Birtaniya Wasanni
  • Tsohon Dan-Takarar Gwamnan PDP A Gombe Ya Shiga ADC Siyasa
  • Masu Ruwa Da Tsaki 60 Sun Samu Horon Sasanta Rikici Don Ƙarfafa Zaman Lafiya Afrika
  • Kungiyoyin Mata A Jihar Filato Sunyi Gangamin Samun Jagorancin Siyasa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.