Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
Published: January 14, 2026 at 3:33 PM | By: Bala Hassan | Updated: January 14, 2026

Shugaban kungiyoyin Magoya Bayan Kwallon Kafa ta Najeriya reshen jihar Bauchi Alh Kabiru Ahmed Vice ya ce Najeriya zata iya samun nasara akan Ƙasar Moroko AFCON 2025.

Alh Kabiru Ahmed Vice ya ce la’akari da yadda tawagar Najeriya suka taka rawar gani a Wasanni su na baya a gasar cin kofin kasashen Afirka tun daga matakin rukuni har zuwa kwata final, haka na nuna cewar zata iya doke masu masaukin baki ƙasar Moroko a wasan da zasuyi na dab da Karshe.

Dukkanin Ƙasashen Afirka da suka je gasar babu wacce ta jefa yawan kwallaye a raga kamar Super Eagles, ” in ji shi.

Wannan ya na da nasaba da irin hazikan yan wasa da suke da su wadda suke fafata a manyan kungiyoyin kwallon kafa ta kasashen turai cikin su hadda wadda suka taba zama Gwarzayen kwallon kafa na afirka guda 2, Victor Osimhen da Ademola Lookman, ganinsu ya kara wa wasu ‘yan wasan karfin guiwa.

Ya ce duk da cewa Ƙasar Moroko ita ce mai masaukin baki ta na da dubban magoya baya a filin hakan ba zai ba ‘yan wasan Najeriya tsoro ba saboda sun goge da irin wannan abu tun a Turai.

Har ila Yau Kabiru yayi kira ga hukumar kwallon kafa ta Najeriya da ta rinka kulawa da walwalan ‘yan wasa da magoya baya don hakan shine zai kara musu kwarin guiwar yin abunda ya dace.

Duk da cewa wannan karon hukumar kwallon kafa ta Najeriya bata mara baya wa bangaren magoya baya don zuwa gasar cin kofin kasashen Afirka da ke guda na a kasar Moroko ba amman suna iya abun da zasuyi don ganin an samu nasara in ji Kabiru.

Saboda haka yayi kira ga gwamnati da masu hanu da shuni da su rinka tallafawa wajan ganin magoya baya suna hallartar irin wa’yannan gasar.

Daga karshe yayi fatan Najeriya zata lashe wannan kofin kasashen Afirka don huce haushin rashin zuwa gasar cin kofin Duniya.

A yau Laraba ne Ƙasar Najeriya zata buga da ƙasar Moroko a matakin wasan dab da Karshe na gasar cin kofin kasashen Afirka AFCON 2025, da ke gudana a can Moroko.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
Next Post: Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi

Karin Labarai Masu Alaka

Umar Aliyu, Shugaban Magoya Bayan Wikki Tourist Jagorancin Wikki Tourist FC Na Samun Yabo Wasanni
Kano Pillars Ta Doke Ikorodu City Wasanni
Chelsea Tayi Kaca-Kaca Da Barcelona A Gasar UCL Wasanni
An Shirya Taron Horas Da Matasa Gabanin Wasan Motsa Jiki 2025 Wasanni
Da Alamu Ronaldo Zai Buga Dukkan Wasanni Da Gasar Kofin Duniya A 2026 Wasanni
Manya-Manyan Wasannin Wannan Makon Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kasar Kenya Zata Samar Da Makamashi Labarai
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Asabar 11.22.2025 Rediyo
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Venezuela Ta Sako Karin Mutanen Da Take Tsare Dasu Labarai
  • Majalisar Dattawa Ta Wanke Janar Christopher Musa A Matsayin Minista Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Chelsea Tayi Kaca-Kaca Da Barcelona A Gasar UCL Wasanni
  • Putin, Sakon Sabuwar Shekara Ya Jinjinawa Dakarun Rasha Da Suke Yaki A Ukraine Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ECOWAS Zata Taimakawa Kasar Benin Da Dakarun Soji Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.