Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

‘Yan Sandan Jihar Bauchi Sun Kama Wasu Matasa da Ake Zargin Su Da Sara Suka 
Published: January 19, 2026 at 9:28 AM | By: Bala Hassan

Rundunan ‘Yan Sandan Jihar Bauchi Ta Kama ‘Yan Sara Suka

An Kama ‘Yan Ta’adda Goma Sha Huɗu (‘Yan Sara-suka) a lokacin wani samame a Bauchi.

Rundunan ta ‘yan sandan jihar Bauchi da ke arewa maso gabas a Najeriya tace a ranar 15 ga Janairu 2026 da misalin ƙarfe hudu da rabi na yammaci, wata sashin sintiri ta yi aiki na kai-kawo kan ayyukan ‘yan ta’adda (‘Yan Sara-suka) a anguwanin Bakaro, Kofar Dumi, Tudun Yarima da Karofin Madaki.

Bayan samun rahoton leken asiri na sirri, jami’in ‘yan sanda na ‘A’ Division Bauchi CSP Hassan A. Musa ya jagoranci wata tawaga da gaggawa inda ya ya cafke wadanda ake zargi da aikata wannan aika-aika, kamar yadda Jami’in hulda da jama’a na ‘yan sandan jihar SP Nafiu Habib, ya bayyana a madadin kwamishinan ‘yan sandan jihar Bauchi Sani Omolori Aliyu.

Wa’yanda aka kama sune.

1. Malam Abbati mai shekaru 20,

2. Malam Mamman mai shekaru 21,

3. Malam Adamu dan shekaru 22,

4. Malam Khalid mai shekaru 20,

5. Malam Abubakar mai shekaru 19,

6. Mr. Mahmood dan shekaru 22,

7. Malam Jabir mai shekaru 21,

8. Malam Haruna mai shekaru 18,

9. Malam Khalid mai shekaru 18,

10. Malam Abubakar dan shekaru 19,

11. Malam Kabiru mai shekaru 20,

12. Malam Anas mai shekaru 20,

13. Malam Mohammed dan shekaru 19,

14. Abdulkarim mai shekaru 22,

Duk kansu daga unguwar Kofar Dumi, Karofin Madaki, Tudun Yarima, da Bakaro, a Bauchi

Wadanda ake zargin sun amsa laifinsu na hada baki a tsakaninsu, inda suke dauke da makamai masu hatsarin gaske da suka hada da wukake masu kaifi, da makamantansu, inda suka mamaye yankunan suka kai musu hari da duka ga al’uma ma zauna unguwar da aka ambata, tare da kwace musu wayoyin hannu da kudi, sannan suka raunata duk wanda ya ki mika musu.

Kwamishinan ‘yan sanda, CP Sani-Omolori Aliyu, ya yabawa al’umar jihar Bauchi bisa hadin kai da goyon bayan da su ke bayarwa, wajan kawo rahoton bata gari, sannan ya karfafa musu gwiwa da su kasance masu taimaka wa jami’an tsaro wajan sanya ido ga masu aikata miyagun hali

Labarai

Post navigation

Previous Post: Kasar Sham Ta Sanar Da Tsagaita Wuta Tsakaninta Da Kungiyar Kurdawa
Next Post: Mutum Mafi Tsufa A Saudiyya Ya Rasu Yana Da Shekaru 142

Karin Labarai Masu Alaka

An Kashe Mutane 169 A Wani Harin Sudan Ta Kudu Afrika
Mabiya Addinin Kirista Da ‘Yan Bindiga Suka Sace Sun Kubuta Labarai
An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026 Afrika
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Masu Zuba Jari A Birnin Paris Afrika
Farashin Mai Ya Cigaba Da Tashi Afrika
Hukumomin Tsaron Najeriya Ne Suka Bukaci Amurka Ta Turo Musu Sojoji Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Kasar Ghana Ta Rage Farashin Cocoa Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Abubakar Malami Bisa Wasu Sharruda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Fara Wata Tattaunawa Afrika
  • Shugaban Trump: Washington Zatayi Cinikayya Da Indiya Amurka
  • Togo Ta Kama Tsohon Shugaban Kasar Burkina Faso Saboda Kitsa Juyin Mulki Afrika
  • Kasar Habasha Ta Cimma Matsaya Da Masu Binta Bashi Afrika
  • Shugabannin Kiristoci Sun Taya Musulmi Murnar Sallah Domin Ƙarfafa Zaman Lafiya Afrika
  • NUJ: Akwai Bukatar Samar Da Inshorar Lafiya Ga ‘Yan Jarida A Najeriya Rediyo
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.