Rundunan ‘Yan Sandan Jihar Bauchi Ta Kama ‘Yan Sara Suka
An Kama ‘Yan Ta’adda Goma Sha Huɗu (‘Yan Sara-suka) a lokacin wani samame a Bauchi.
Rundunan ta ‘yan sandan jihar Bauchi da ke arewa maso gabas a Najeriya tace a ranar 15 ga Janairu 2026 da misalin ƙarfe hudu da rabi na yammaci, wata sashin sintiri ta yi aiki na kai-kawo kan ayyukan ‘yan ta’adda (‘Yan Sara-suka) a anguwanin Bakaro, Kofar Dumi, Tudun Yarima da Karofin Madaki.
Bayan samun rahoton leken asiri na sirri, jami’in ‘yan sanda na ‘A’ Division Bauchi CSP Hassan A. Musa ya jagoranci wata tawaga da gaggawa inda ya ya cafke wadanda ake zargi da aikata wannan aika-aika, kamar yadda Jami’in hulda da jama’a na ‘yan sandan jihar SP Nafiu Habib, ya bayyana a madadin kwamishinan ‘yan sandan jihar Bauchi Sani Omolori Aliyu.
Wa’yanda aka kama sune.
1. Malam Abbati mai shekaru 20,
2. Malam Mamman mai shekaru 21,
3. Malam Adamu dan shekaru 22,
4. Malam Khalid mai shekaru 20,
5. Malam Abubakar mai shekaru 19,
6. Mr. Mahmood dan shekaru 22,
7. Malam Jabir mai shekaru 21,
8. Malam Haruna mai shekaru 18,
9. Malam Khalid mai shekaru 18,
10. Malam Abubakar dan shekaru 19,
11. Malam Kabiru mai shekaru 20,
12. Malam Anas mai shekaru 20,
13. Malam Mohammed dan shekaru 19,
14. Abdulkarim mai shekaru 22,
Duk kansu daga unguwar Kofar Dumi, Karofin Madaki, Tudun Yarima, da Bakaro, a Bauchi
Wadanda ake zargin sun amsa laifinsu na hada baki a tsakaninsu, inda suke dauke da makamai masu hatsarin gaske da suka hada da wukake masu kaifi, da makamantansu, inda suka mamaye yankunan suka kai musu hari da duka ga al’uma ma zauna unguwar da aka ambata, tare da kwace musu wayoyin hannu da kudi, sannan suka raunata duk wanda ya ki mika musu.
Kwamishinan ‘yan sanda, CP Sani-Omolori Aliyu, ya yabawa al’umar jihar Bauchi bisa hadin kai da goyon bayan da su ke bayarwa, wajan kawo rahoton bata gari, sannan ya karfafa musu gwiwa da su kasance masu taimaka wa jami’an tsaro wajan sanya ido ga masu aikata miyagun hali


