Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka

‘Yan Sandan Jihar Bauchi Sun Kama Wasu Matasa da Ake Zargin Su Da Sara Suka 
Published: January 19, 2026 at 9:28 AM | By: Bala Hassan

Rundunan ‘Yan Sandan Jihar Bauchi Ta Kama ‘Yan Sara Suka

An Kama ‘Yan Ta’adda Goma Sha Huɗu (‘Yan Sara-suka) a lokacin wani samame a Bauchi.

Rundunan ta ‘yan sandan jihar Bauchi da ke arewa maso gabas a Najeriya tace a ranar 15 ga Janairu 2026 da misalin ƙarfe hudu da rabi na yammaci, wata sashin sintiri ta yi aiki na kai-kawo kan ayyukan ‘yan ta’adda (‘Yan Sara-suka) a anguwanin Bakaro, Kofar Dumi, Tudun Yarima da Karofin Madaki.

Bayan samun rahoton leken asiri na sirri, jami’in ‘yan sanda na ‘A’ Division Bauchi CSP Hassan A. Musa ya jagoranci wata tawaga da gaggawa inda ya ya cafke wadanda ake zargi da aikata wannan aika-aika, kamar yadda Jami’in hulda da jama’a na ‘yan sandan jihar SP Nafiu Habib, ya bayyana a madadin kwamishinan ‘yan sandan jihar Bauchi Sani Omolori Aliyu.

Wa’yanda aka kama sune.

1. Malam Abbati mai shekaru 20,

2. Malam Mamman mai shekaru 21,

3. Malam Adamu dan shekaru 22,

4. Malam Khalid mai shekaru 20,

5. Malam Abubakar mai shekaru 19,

6. Mr. Mahmood dan shekaru 22,

7. Malam Jabir mai shekaru 21,

8. Malam Haruna mai shekaru 18,

9. Malam Khalid mai shekaru 18,

10. Malam Abubakar dan shekaru 19,

11. Malam Kabiru mai shekaru 20,

12. Malam Anas mai shekaru 20,

13. Malam Mohammed dan shekaru 19,

14. Abdulkarim mai shekaru 22,

Duk kansu daga unguwar Kofar Dumi, Karofin Madaki, Tudun Yarima, da Bakaro, a Bauchi

Wadanda ake zargin sun amsa laifinsu na hada baki a tsakaninsu, inda suke dauke da makamai masu hatsarin gaske da suka hada da wukake masu kaifi, da makamantansu, inda suka mamaye yankunan suka kai musu hari da duka ga al’uma ma zauna unguwar da aka ambata, tare da kwace musu wayoyin hannu da kudi, sannan suka raunata duk wanda ya ki mika musu.

Kwamishinan ‘yan sanda, CP Sani-Omolori Aliyu, ya yabawa al’umar jihar Bauchi bisa hadin kai da goyon bayan da su ke bayarwa, wajan kawo rahoton bata gari, sannan ya karfafa musu gwiwa da su kasance masu taimaka wa jami’an tsaro wajan sanya ido ga masu aikata miyagun hali

Labarai

Post navigation

Previous Post: Kasar Sham Ta Sanar Da Tsagaita Wuta Tsakaninta Da Kungiyar Kurdawa
Next Post: Mutum Mafi Tsufa A Saudiyya Ya Rasu Yana Da Shekaru 142

Karin Labarai Masu Alaka

An Bude Kamfanin Sarrafa Ma’adanai A Kasar Mozambique Labarai
Margayi Shugaba Muhammadu Buhari 1942-2025 Labarai
Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana Afrika
Akwai Nasara A Tattaunawar Da Akeyi Tsakanin Iran Da Amurka Afrika
An Gudanar Da Addu’o’i Na Musamman Don Neman Zaman Lafiya Labarai
Tsohon Alkalin Alkalai A Najeriya Ya Rasu Yana Da Shekaru 71 Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga
  • Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030
  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Hadakar Gwamnatin Najeriya Da Amurka Ne Suka Kai Hari Sokoto Najeriya
  • Gwamnatin Amurka Da Najeriya Sunyi Hadakar Inganta Asibiticin Kiristoci Amurka
  • Chelle: Rashin Jituwa Tsakanin Osimhen Da Lookman Matsala Ce Ta Cikin Gida Wasanni
  • Gwamnan Jihar Filato Na Shirin Komawa APC Siyasa
  • Gwamna Ahmad Aliyu Na Jihar Sokoto Ya Gabatar Da Kasafin Fiye Da Naira Biliyan 700 Labarai
  • An Gano Wani Kurkukun Sirri Da Ake Azaftar Da Mutane A Kasar Libya Afrika
  • Gwamnatin Kano Zata Dauki Mataki Game Da Kisan Dorayi Tsaro
  • Shugaban Kasar Ivory Coast Yayi Sauye-Sauye A Majalisar Ministocin Kasar Siyasa
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.