Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Dakarun Gwamnatin Kasar Sham Tayi Mamaya Zuwa Gabashin Kasar
Published: January 19, 2026 at 5:48 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Dakarun gwamnatin kasar Sham sun kame lardukan da ke arewaci da gabashin kasar gam bayan ficewar dakarun kurdawa cikin gaggawa, a wani yanayi da ya bada mamaki, wanda kuma ya kara karfafa mulkin shugaba Ahmed al-Sharaa.

Dakarun kurdawa sun yarda da ficewa daga yankunan Aleppo, da suka dade suna rike da madafun ikon su, har da wurare masu arzikin man fetur, ranar Lahadi bayan da aka shafe kwanaki ana gwabza kazamin fada tsakanin su da dakarun gwamnati.

Amma duk da Wannan matsayar da aka cimma don kawo zaman lafiya, rahotanni sun nuna cewa An ci gaba da gwabza fada ranar Litinin.

Dakarun kurdawa na SDF sun watsu dauke da Makamai sun far ma wani gidan kurkuku da suke tsare da dubbannin ‘yan kungiyar ta’adda na ISIS, ba tare da sun fadi sunan wadanda suka kai harin ba. Kurdawan sun kara da cewa suna Karawa da dakarun gwamnati kusa da wani kurkukun da ke dauke da ‘yan ISIS kusa da garin Raqqa.

A nasu bangaren, sojojin Syria sun zargi dakarun Kurdawan da neman kawo koma baya a yarjejeniyar da aka yi, inda suka ce An kashe sojojin su 3 a fadan na kwanan nan

Labarai

Post navigation

Previous Post: Sojin Kasar Congo Da ‘Yan Tawaye Sun Kara Shiga Yankin Uvira
Next Post: Shugaban Amurka Donald Trump Ya Jadda da Kudirinsa Da Kwace Iyakar Greenland

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamna Ahmad Aliyu Na Jihar Sokoto Ya Gabatar Da Kasafin Fiye Da Naira Biliyan 700 Labarai
Baitul Malin Amurka Zata Bawa Venezuela Da Cuba Damar Sayar Da Mai Amurka
Nuhu Ribadu Ya Mika Dalibai 100 da Aka Ceto Ga Gwamnatin Jihar Neja Labarai
Muna Kokarin Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Gombe – Uwargidan Gwamna Labarai
Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya Afrika
Majalisar Dokokin Kamaru Ta Amince Da Wasu Sauye Sauye Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Rahoton MDD Yace An Kashe Fiye Da Farar 1000 A Sudan Labarai
  • Wani Alkali A Amurka Ya Kalubalanci Gwamnatin Kasar Afrika
  • Sakamakon Rikicin Gabas Ta Tsakiya Farashin Mai Ya Karu Labarai
  • Hukumar Hakar Ma’adanai A Kasar Zambiya Ta Dakatar Da Ayyukanta Kimiya
  • Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Harin Jos Afrika
  • Iran Tace Dole A Tsagaita Wuta A Lebanon Kafun Fara Shawarwari Amurka
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 50 Tare Da Sace Mata Da Yara A Jihar Zamfara Najeriya
  • Dakarun Sakai A Kasar Sudan Sun Kashe Mutane 28 A Wani Farmaki Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.