Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Masu Tayar Da Hankali
Published: January 24, 2026 at 9:24 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Babban Hafsan Sojin Ƙasarln Najeriya, Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya yi gargaɗi mai tsanani ga masu aikata laifuka da ke tayar da hankalin al’umma a faɗin ƙasar, inda ya ce za su fuskanci ƙarfin sojoji matuƙar ba su tuba daga munanan ayyukansu ba.

Fiye da sojojin musamman dubu ɗaya (1,000) ne aka ƙara tura wa fagen yaƙi domin ƙarfafa ayyukan tsaron cikin gida da ake gudanarwa a sassa daban-daban na ƙasar.

Babban Hafsan Sojin ya bayyana hakan ne yayin bikin kammala atisayen Exercise Restore Hope 9 da aka gudanar a sansanin rundunar sojin Najeriya da ke Kachia.

Ya jaddada cewa rundunar sojin ƙasa za ta ci gaba da tinkarar duk wani ɓangare na masu tada fitina, inda ya ce duk masu aikata laifi za su gamu da ƙarfin da za su iya jurewa, har sai sun daina munanan ayyukansu kuma sun tuba.

Ya kuma tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa rundunar sojin ƙasa za ta ci gaba da jajircewa wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Gwamna Ododo Ya Gargadi Sarakunan Gargajiya
Next Post: Najeriya Da Amurka Sun Amince Su Haɗa Kai Don Inganta ’Yancin Addini Da ƙarfafa Tsaro A Nijeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Dangote Ya Rage Farashin Mai A Najeriya Labarai
Yanbindiga sun Kashe kimanin mutane 30 a yankin kayama ta Jihar kwaran Najeriya Najeriya
An Kaddamar Da Kwamitin Kwallon Kafa A Tsakanin Masarautun Jihar Gombe Labarai
Ma’aikatan Tattara Kudin Haraji Sunyi Rikici Da Masu Babura A Bauchi Najeriya
An Tsinci Gawar Yarinya A Gombe Najeriya
Gwamnatin Kano: Zamu Kara Daukar Malamai Domin Inganta Ilimi Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga
  • Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030
  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo
  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Masu Kare Hakkin ‘Yan Gudun Hijira A Amurka Sun Mika Koke Amurka
  • Gobara Ta Tashi A Makarantar Koyon Jinyar Dabbobi Dake Jihar Kano Najeriya
  • Jirgin Sojojin Ruwa Yayi Gobara A Cross River Najeriya
  • Wani Harin ‘Yan Bindiga Ya Kashe Mutane 35 A Jihar Borno Labarai
  • Fadar Shugaban Ƙasan Najeriya Ta Musanta Wani Labarin ƙarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya: Ba Don Leken Asiri Muka Tura Jirgin Yakin Mu Ba Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • AFCON 2025, Jerin Abubuwan Da Aka Haramta Wa Magoya Baya Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.