Gwamnatin jihar Kano ta bayyana cewa za a warware rikicin masarautar anan kusa.
Kwamishinan yaɗa labarai da harkokin cikin gida na jihar, Ibrahim Waiya, ne ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai a ranar Alhamis a Kano.
Waiya ya tabbatar wa al’ummarl cewa an riga an ɗauki tsare-tsare masu ƙarfi domin dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali mai ɗorewa a Kano.
Ya ce gwamnatin jihar na da ƙudirin yin tattaunawa da dukkan masu ruwa da tsaki, inda ya jaddada cewa gwamnatin ta himmatu wajen tabbatar da cewa batun masarautar bai ci gaba da haifar da tashin hankali ko kawo cikas ga harkokin mulki ba.
A cewarsa, tsarin da gwamnati ke bi yana karkashin mutunta dokokin ƙasa, darajar sarakunan gargajiya, da kuma muradun bai ɗaya na al’ummar Jihar Kano.


