A cikin makon nan gwamnatin shugaba Trump tana ganawa da manyan jami’an tsaron aikin leken asiri daga Isra’ila da saudiyya, a Washington DC domin tattaunawa a zama daban daban game da Iran, yayinda shugaba Trump yake tunanin kaiwa Farisan farmaki, kamar yadda wasu majiyoyi da suke da sanayya kan lamarin suka fada.
Zaman dar dar ya karu a gabas ta tsakiya sakamakon jibge kayan yaki a yankin da Amurka take yi. Ranar laraba shugaba Trump yayi kira ga Iran ta hanzarta zuwa teburin shawarwari kan shirin Nukiliyar kasar, ko ta fuskanci farmaki daga Amuka. Wanda yasa Iran kuma tayi barazanar daga Iran cewa zata maida martani mai tsanani idan aka taba ta.
Kamar yadda wasu kafofin yada labarai na Amurka suka bayyana, babban jami’in aikin leken asiri na Isra’ila Janar Shlomi Binder, yayi shawarwari da jami’an Amurka a ma’aikatar tsaro ta Pentagon, da CIA, da kuma fadar White House a ranakun talata da laraba, inda ya gabatar da bayanai kan wasu muhimman wurare da Amurka zata iya aunawa idan ta tsaida shawarar kai wa Iran din hari.
Haka nan shima Ministan harkokin tsaro na Saudiyya Yerima Khalid Bin Salman, yana Birnin Washington domin gudanar da shawarwari da Washington akan batun na Iran.
Saudiyya da wasu kasashe da suke yankin Gulf, sun nemi sassauta lamarin domin kaucewa yaki da zai shafi yankin na gabas ta tsaiya baki daya.


