Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Amurka Tana Ganawa Da Manyan Jami’an Leken Asiri
Published: January 30, 2026 at 9:57 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

A cikin makon nan gwamnatin shugaba Trump tana ganawa da manyan jami’an tsaron aikin leken asiri daga Isra’ila da saudiyya, a Washington DC domin tattaunawa a zama daban daban game da Iran, yayinda shugaba Trump yake tunanin kaiwa Farisan farmaki, kamar yadda wasu majiyoyi da suke da sanayya kan lamarin suka fada.

Zaman dar dar ya karu a gabas ta tsakiya sakamakon jibge kayan yaki a yankin da Amurka take yi. Ranar laraba shugaba Trump yayi kira ga Iran ta hanzarta zuwa teburin shawarwari kan shirin Nukiliyar kasar, ko ta fuskanci farmaki daga Amuka. Wanda yasa Iran kuma tayi barazanar daga Iran cewa zata maida martani mai tsanani idan aka taba ta.

Kamar yadda wasu kafofin yada labarai na Amurka suka bayyana, babban jami’in aikin leken asiri na Isra’ila Janar Shlomi Binder, yayi shawarwari da jami’an Amurka a ma’aikatar tsaro ta Pentagon, da CIA, da kuma fadar White House a ranakun talata da laraba, inda ya gabatar da bayanai kan wasu muhimman wurare da Amurka zata iya aunawa idan ta tsaida shawarar kai wa Iran din hari.

Haka nan shima Ministan harkokin tsaro na Saudiyya Yerima Khalid Bin Salman, yana Birnin Washington domin gudanar da shawarwari da Washington akan batun na Iran.

Saudiyya da wasu kasashe da suke yankin Gulf, sun nemi sassauta lamarin domin kaucewa yaki da zai shafi yankin na gabas ta tsaiya baki daya.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Sojan Burkina Faso Ta Soke Jam’iyyun Siyasar Kasar
Next Post: An Maka Wasu Jami’an Immigration A Kotu Bisa Zargin Rashin Da’a A Birtaniya

Karin Labarai Masu Alaka

Ministan Kudin Botswana Yace Akwai Hasashen Cewa Tattalin Arzikin Kasar Zai Ragu Amurka
Shugaba Trump Yayi Barazanar Tura Sojoji Ga Masu Zanga Zanga Amurka
Iran Ta Kama Wasu ‘Yan Leken Asiri Afrika
Kasashen Da Suke Kawance Da Amurka Sun Juyawa Trump Baya Afrika
Shugaban Amurka Zai Sake Gine Gaza Amurka
Shugaban Amurka Yace Zayyi Wahala A Cimma Yarjejeniya Tsakanin Isra’ila, Amurka Da Iran Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gaza Ga Albarusai Ga Yunwa Tsaro
  • Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya Afrika
  • Shugaban Majalisar Tarayyar Turai Yace Rasha Tana Cin Ribar Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Jami’an tsaro sama da dubu biyar ne zasuyi aikin tabbatar da tsaro Alokacin bikin karamar sallah a Jihar Nejan Najeriya. Najeriya
  • Majalisa Ta Sanya Baki Akan Rikici Tsakanin Dangote Da Hukumar Albarkatun Mai Najeriya
  • Amurka Ta Gabatarwa Sassan Dake Yakar Juna A Sudan da Shirin Tsagaita Wuta Afrika
  • Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Kasafin Kudi Mai Sauya Fasali Da Karfafa Rayuwar Al’umma Labarai
  • Shugaban Amurka Yayi Watsi Da Tattaunawar Kawo Karshen Yaki Da Iran Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.