Ahalinda ake ciki kuma, kasashe biyar sun amince zasu tura sojoji domin ayyukan kiyaye zaman lafiya a Gaza, kamar yadda kwamandan rundunar manjo janar Jeff Jeffers na sojin Amurka ya fada a lokacin taron kwamitin wanzar da zaman lafiya, da shugaban Amurka Donald Trump ya kafa.
Kasashe biyar na farko da suka amince za su tura sojoji domin aikin kiyaye zaman lafiyan sun hada da Indonesia, da Morocco, da Kazakhsatan, da Kosovo, da Albania. Wasu kasashe biyu kuma Masar da Jordan, sunyi alkawarin za su horasda jami’an ‘Yan sanda.
Janar Jeffers yace rundunar zata fara aiki ne wajen tura sojojin zuwa Rafah dake Kudancin Gaza, ta horasda ‘yan sanda sannan su bi aikin sashe da sashe.


